< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Tacker Herranom, och prediker hans Namn; förkunner hans verk ibland folken.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sjunger om honom, och lofver honom; taler om all hans under.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Lofver hans helga Namn; deras hjerta, som Herran söka, glädje sig.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Fråger efter Herranom, och efter hans magt; söker hans ansigte alltid.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Tänker uppå hans underliga verk, som han gjort hafver; uppå hans under, och uppå hans ord;
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
I Abrahams hans tjenares säd, I Jacobs hans utkorades barn.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Han är Herren vår Gud; han dömer i hela verldene.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Han tänker evinnerliga uppå sitt förbund; på det ord han lofvat hafver till mång tusend, slägte ifrå slägte;
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Det han gjort hafver med Abraham; och på eden med Isaac;
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Och satte det Jacob till en rätt, och Israel till ett evigt förbund;
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Och sade: Dig vill jag gifva det landet Canaan, edars arfs lott;
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Då de få och ringa voro, och främlingar derinne.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Och de foro ifrå folk till folk; ifrå det ena riket till annat folk.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Han lät ingen menniska göra dem skada, och näpste Konungar för deras skull:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Kommer intet vid mina smorda, och görer intet ondt minom Prophetom.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Och han lät en dyr tid komma i landet, och förtog dem allt bröds uppehälle.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Han sände en man framför dem; Joseph vardt såld till en träl.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
De tvingade hans fötter i fjettrar; hans kropp måste jern ligga;
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Tilldess hans ord kom, och Herrans tal pröfvade honom.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Då sände Konungen bort, och lät gifva honom lös; herren öfver folken böd låta honom ut.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Han satte honom till en herra öfver sitt hus; till en föreståndare öfver alla sina ägodelar;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Att han skulle undervisa hans Förstar, efter sitt sätt, och lära hans äldsta vishet.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Och Israel for in uti Egypten, och Jacob vardt en främling i Hams land.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Och han lät sitt folk svåliga växa, och gjorde dem mägtigare än deras fiender.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Han förvände deras hjerta, så att de hans folk hätske vordo, och tänkte till att förtrycka hans tjenare med list.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Han sände sin tjenare Mose; Aaron, den han utvalt hade.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
De samme gjorde hans tecken ibland dem, och hans under i Hams land.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Han lät mörker komma, och gjordet mörkt; och de voro icke hans ordom ohörsamme.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Han förvände deras vatten i blod, och dräp deras fiskar.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Deras land gaf myckna paddor ifrå sig; ja, uti deras Konungars kamrar.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Han sade, då kom ohyra; löss uti alla deras landsändar.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Han gaf dem hagel till regn; eldslåga uti deras land;
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Och slog deras vinträ och fikonaträ, och förderfvade trän i deras landsändar.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Han sade, då kommo gräshoppor, gräsmatkar otalige;
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Och de uppåto allt gräset i deras land, och uppfrätte frukten på deras mark;
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Och slog allt förstfödt uti deras land, alla deras första arfvingar.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Och han förde dem ut med silfver och guld, och ibland deras slägter var ingen krank.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypten var glad, att de utdrogo; ty deras fruktan var uppå dem fallen.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Han utsträckte en molnsky till skjul, och eld om nattena till att lysa.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
De bådo, och han lät komma åkerhöns; och han mättade dem med himmelsbröd.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Han öppnade bergsklippona, och vatten flöt derut, så att bäcker flöto i torra öknene.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Ty han tänkte på sitt helga ord, det han till Abraham sin tjenare talat hade.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Alltså förde han sitt folk ut med fröjd, och sina utkorade med glädje;
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Och gaf dem Hedningarnas land, så att de folks gods intogo;
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
På det de skulle hålla hans rätter, och bevara hans lag. Halleluja.

< Zabura 105 >