< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Mshukuruni Yahwe, liitieni jina lake; myafanye matendo yake yajulikane kati ya mataifa.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Mwimbieni yeye, mwimbieni sifa yeye; semeni matendo yake yote ya ajau.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Mjivune katika utakatifu wa jina lake; moyo wao wamtafutao Yahwe ufurahi.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Mtafuteni Yahwe na nguvu zake; utafuteni uwepo wake siku zote.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Kumbukeni mambo ya ajabu aliyoyatenda,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
miujiza yake na amri zitokazo kinywani mwake, enyi kizazi cha Ibrahimu mtumishi wake, enyi watu wa Yakobo, wachaguliwa wake.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Yeye ni Yahwe, Mungu wetu. Amri zake ziko juu ya nchi yote.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Naye hulikumbuka agano lake milele, neno alilo amuru kwa ajili ya vizazi elfu.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Hulikumbuka agano alilolifanya na Ibrahimu na kiapo alicho mwapia Isaka.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Hiki ndicho alicho mthibitishia Yakobo kama agano na kama agano la milele kwa Israeli.
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Alisema, “Nitakupa wewe ardhi ya Kanaani kama sehemu yako ya urithi.”
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Alisema hili wakati tu walipokuwa wachache katika hesabu, yaani wachahe sana, nao walikuwa wageni katika nchi.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Walienda taifa hadi taifa na kutoka ufalme moja kwenda mwingine.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Hakuruhusu yeyote kuwaonea; aliwakemea wafalme kwa ajili yao.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Alisema, “Msiwaguze wapakwa mafuta wangu, na msiwadhuru manabii wangu.”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Aliita njaa katika nchi; akaondoa upatikanaji wa mkate wote.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Akatuma mtu mbele yao; Yusufu aliuzwa kama mtumishi.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Miguu yake ilifungwa kwa pingu; alivishwa mnyororo wa chuma shingoni mwake,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
mpaka wakati wa maneno yake ulipotimia, nalo neno la Yahwe lilimjaribu.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Mfalme alituma watumishi kumfungua; mtawala wa watu alimuweka huru.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Alimuweka kuwa msimamizi wa nyumba yake kama mtawala wa mali zake zote
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
kuwaelekeza wakuu kama alivyopenda na kuwafundisha viongozi wake hekima.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Kisha Israeli iliingia Misri, na Yakobo aliishi kwa muda katika nchi ya Hamu.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Yahwe aliwajalia watu wake wazae sana, na aliwafanya wenye nguvu kuliko adui zao.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Alisababisha adui zao wawachukie watu wake, na kuwatendea visivyo watumishi wake.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Alimtuma Musa, mtumishi wake, na Haruni, ambaye alikwisha mchagua.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Walifanya ishara zake kati ya Wamisri na maajabu yake katika ya nchi ya Hamu.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Alituma giza na likaifanya nchi hiyo kuwa giza, lakini watu wake hawakutii amri zake.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Aligeuza maji kuwa damu na aliua samaki wao.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Nchi yao ilijaa vyura, hata katika vyumba vya watawala wao.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Alisema, na makundi ya inzi na chawa wakaja mjini mwote.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Aliigeuza mvua yao kuwa mvua ya mawe, pamoja na miali ya moto juu ya ardhi yao.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Aliiharibu mizabibu yao na mitini yao; akaivunja miti ya mji wao.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Alisema, na nzige wakaja, nzige wengi sana.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Nzige walikula mboga zao zote za majani katika nchi yao. Walikula mazao yote ardhini.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Aliua kila mzaliwa wa kwanza katika nchi yao, malimbuko ya nguvu zao.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Aliwatoa nje Waisraeli wakiwa na fedha na dhahabu; hakuna mmoja wa kabila lake aliyejikwaa njiani.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Misri ilifurahi walipoondoka, maana Wamisri waliwaogopa.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Alitandaza wingu liwafunike na alifanya moto uwaangazie wakati wa usiku.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Waisraeli waliomba chakula, naye aliwaletea kware na aliwatosheleza kwa mkate kutoka mbiguni.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Aliugawa mwamba, maji yalimwagika kutoka humo; yalitiririka katika jangwa kama mto.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Kwa maana alikumbuka ahadi yake takatifu aliyoifanya kwa Ibrahimu mtumishi wake.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Aliwaongoza watu wake kwa furaha, wateule wake kwa kelele za ushindi.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Aliwapa nchi za mataifa; walichukua milki ya mali za watu
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
ili waweze kushika amri zake na kutii sheria zake. Msifuni Yahwe.

< Zabura 105 >