< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
¡Denle gracias al Señor, alaben su maravillosa naturaleza! ¡Que todo el mundo sepa lo que Él ha hecho!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
¡Cántenle a él, canten alabanzas; cuéntenle a todos las grandes cosas que ha hecho!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Siéntanse orgullosos de su santo nombre; alégrense, todos los que vienen al Señor!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Busquen al Señor, y a su fuerza; busquen siempre estar en su presencia.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Recuerden las maravillas que ha creado, los milagros que ha hecho, y los juicios que ha llevado a cabo,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
descendientes de Abraham, hijos de Israel, su pueblo escogido.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Él es el Señor, Nuestro Dios, sus juicios cubren toda la tierra!
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Él siempre recuerda su pacto, la promesa que ha hecho durará por mil generaciones;
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
el pacto que hizo con Abraham, el voto que le dio a Isaac.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
El Señor lo confirmó a Jacob con un decreto, hizo este acuerdo de unión con Israel:
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
diciendo, “Te daré la tierra de Canaán”.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Él dijo esto cuando aún eran solo unos pocos, solo un pequeño grupo de extranjeros en la tierra.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Vagaban de nación en nación, de un reino a otro.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Pero Él no permitió que nadie los tratara mal; advirtiendo a los reyes que los dejarán en paz:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
“No coloques mano sobre mi pueblo escogido, ni le hagas daño a mis profetas!”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Causó una hambruna en la tierra de Canaán para que no hubiera comida.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Pero, antes de eso envió a un hombre, José, quién había sido vendido como un esclavo.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Hirieron sus pies al ponerle cadenas, y pusieron un collar de hierro alrededor de su cuello,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
hasta que el tiempo predicho llegó cuando el Señor lo probó.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
El rey envió por él y lo liberó; el rey del pueblo lo dejó en libertad.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Puso a José a cargo de la casa real, a cargo de todo lo que tenía,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
para que le enseñara a los oficiales del rey todo lo que él quisiera, para hacer más sabios a los consejeros del rey.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Entonces Israel vino a Egipto, Jacob se estableció como extranjero en la tierra de Cam.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
El Señor hizo a su pueblo más fuerte y más fértil que a sus enemigos.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Hizo que los egipcios cambiaran de opinión y odiarán a su gente.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Envió a su siervo Moisés, junto con Aarón, a quienes había escogido.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Llevaron sus señales milagrosas a los egipcios, sus maravillas hasta la tierra de Cam.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Hundió la nación en densas tinieblas, porque ¿acaso no se habían opuesto a lo que el Señor había dicho?
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Él convirtió su agua en sangre, matando a todos los peces.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Luego envió una plaga de ranas a todo el país que entraban hasta a los cuartos de los gobernadores.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Dio la orden, y las moscas se esparcieron por toda la tierra; los mosquitos estaban por todas partes.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Hizo llover granizo sobre ellos, y relámpagos sobre todo el país.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Destruyó sus cultivos de vino, y acabó con sus árboles.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Dio la orden, y los enjambres de langostas vinieron, miles y miles de langostas:
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
ellas se comieron toda la vegetación sobre la tierra; terminaron con todos los cultivos.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Dios mató a todos los primogénitos de Egipto, el primero en ser concebido en toda su fuerza y vigor.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Y entonces guió a su pueblo fuera de Egipto, llevando consigo plata y oro, y ninguna de las tribus tambaleó.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Los egipcios se alegraron de su partida, porque tenían miedo de los Israelitas.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
El Señor mandó una nube sobre ellos como cubierta, y en la noche, una columna de fuego para darles luz.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Les dios codornices para comer cuando se lo pidieron; los alimentó con el pan del cielo hasta que estuvieron saciados.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Abrió la roca, y el agua comenzó a fluir, un río en medio del desierto.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Porque él recordó su pacto santo con su siervo Abraham.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Así que liberó a su pueblo, sus elegidos, mientras cantaban de alegría.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Les dio las tierras de las naciones paganas, y heredaron todo aquello por cuanto los demás habían trabajado.
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
El Señor hizo esto para que ellos lo siguieran y guardaran sus leyes. ¡Alaben al Señor!