< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Louvae ao Senhor, e invocae o seu nome; fazei conhecidas as suas obras entre os povos.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Cantae-lhe, cantae-lhe psalmos: fallae de todas as suas maravilhas.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Gloriae-vos no seu sancto nome: alegre-se o coração d'aquelles que buscam ao Senhor.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Buscae ao Senhor e a sua força: buscae a sua face continuamente.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Lembrae-vos das maravilhas que fez, dos seus prodigios e dos juizos da sua bocca;
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Vós, semente d'Abrahão, seu servo, vós, filhos de Jacob, seus escolhidos.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Elle é o Senhor, nosso Deus; os seus juizos estão em toda a terra.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Lembrou-se do seu concerto para sempre, da palavra que mandou a milhares de gerações.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
O qual concerto fez com Abrahão, e o seu juramento a Isaac.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
E confirmou o mesmo a Jacob por estatuto, e a Israel por concerto eterno,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Dizendo: A ti darei a terra de Canaan, a sorte da vossa herança.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Quando eram poucos homens em numero, sim, mui poucos e estrangeiros n'ella.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Quando andavam de nação em nação e d'um reino para outro povo.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Não permittiu a ninguem que os opprimisse, e por amor d'elles reprehendeu a reis, dizendo:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Não toqueis os meus ungidos, e não maltrateis os meus prophetas.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Chamou a fome sobre a terra, quebrantou todo o sustento do pão.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Mandou perante elles um varão, José, que foi vendido por escravo:
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Cujos pés apertaram com grilhões: foi mettido em ferros:
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Até ao tempo em que chegou a sua palavra; a palavra do Senhor o provou.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Mandou o rei, e o fez soltar; o governador dos povos, e o soltou.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Fel-o senhor da sua casa, e governador de toda a sua fazenda;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Para sujeitar os seus principes a seu gosto, e instruir os seus anciãos.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Então Israel entrou no Egypto, e Jacob peregrinou na terra de Cão.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
E augmentou o seu povo em grande maneira, e o fez mais poderoso do que os seus inimigos.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Virou o coração d'elles para que aborrecessem o seu povo, para que tratassem astutamente aos seus servos.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Enviou Moysés, seu servo, e Aarão, a quem escolhera.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Mostraram entre elles os seus signaes e prodigios, na terra de Cão.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Mandou trevas, e a fez escurecer; e não foram rebeldes á sua palavra.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Converteu as suas aguas em sangue, e matou os seus peixes.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
A sua terra produziu rãs em abundancia, até nas camaras dos seus reis.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Fallou elle, e vieram enxames de moscas e piolhos em todo o seu termo.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Converteu as suas chuvas em saraiva, e fogo abrazador na sua terra.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Feriu as suas vinhas e os seus figueiraes, e quebrou as arvores dos seus termos.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Fallou elle, e vieram gafanhotos e pulgão sem numero.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
E comeram toda a herva da sua terra, e devoraram o fructo dos seus campos.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Feriu tambem a todos os primogenitos da sua terra, as primicias de todas as suas forças.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
E tirou-os para fóra com prata e oiro, e entre as suas tribus não houve um só fraco.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
O Egypto se alegrou quando elles sairam, porque o seu temor caira sobre elles.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Estendeu uma nuvem por coberta, e um fogo para alumiar de noite.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Oraram, e elle fez vir codornizes, e os fartou de pão do céu.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Abriu a penha, e d'ella correram aguas; correram pelos logares seccos como um rio.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Porque se lembrou da sua sancta palavra, e de Abrahão, seu servo.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
E tirou d'ali o seu povo com alegria, e os seus escolhidos com regozijo.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
E deu-lhes as terras das nações; e herdaram o trabalho dos povos;
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Para que guardassem os seus preceitos, e observassem as suas leis. Louvae ao Senhor.