< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
alleluia confitemini Domino et invocate nomen eius adnuntiate inter gentes opera eius
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
cantate ei et psallite ei narrate omnia mirabilia eius
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
laudamini in nomine sancto eius laetetur cor quaerentium Dominum
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
quaerite Dominum et confirmamini quaerite faciem eius semper
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
mementote mirabilium eius quae fecit prodigia eius et iudicia oris eius
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
semen Abraham servi eius filii Iacob electi eius
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
ipse Dominus Deus noster in universa terra iudicia eius
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
memor fuit in saeculum testamenti sui verbi quod mandavit in mille generationes
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
quod disposuit ad Abraham et iuramenti sui ad Isaac
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
et statuit illud Iacob in praeceptum et Israhel in testamentum aeternum
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
dicens tibi dabo terram Chanaan funiculum hereditatis vestrae
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
cum essent numero breves paucissimos et incolas eius
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
et pertransierunt de gente in gentem et de regno ad populum alterum
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
non reliquit hominem nocere eis et corripuit pro eis reges
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
nolite tangere christos meos et in prophetis meis nolite malignari
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
et vocavit famem super terram omne firmamentum panis contrivit
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
misit ante eos virum in servum venundatus est Ioseph
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
humiliaverunt in conpedibus pedes eius ferrum pertransiit anima eius
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
donec veniret verbum eius eloquium Domini inflammavit eum
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
misit rex et solvit eum princeps populorum et dimisit eum
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
constituit eum dominum domus suae et principem omnis possessionis suae
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
ut erudiret principes eius sicut semet ipsum et senes eius prudentiam doceret
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
et intravit Israhel in Aegyptum et Iacob accola fuit in terra Cham
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
et auxit populum eius vehementer et firmavit eum super inimicos eius
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
convertit cor eorum ut odirent populum eius ut dolum facerent in servos eius
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
misit Mosen servum suum Aaron quem elegit ipsum
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
posuit in eis verba signorum suorum et prodigiorum in terra Cham
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
misit tenebras et obscuravit et non exacerbavit sermones suos
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
convertit aquas eorum in sanguinem et occidit pisces eorum
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
dedit terra eorum ranas in penetrabilibus regum ipsorum
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
dixit et venit cynomia et scinifes in omnibus finibus eorum
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
posuit pluvias eorum grandinem ignem conburentem in terra ipsorum
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
et percussit vineas eorum et ficulneas eorum et contrivit lignum finium eorum
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
dixit et venit lucusta et bruchus cuius non erat numerus
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
et comedit omne faenum in terra eorum et comedit omnem fructum terrae eorum
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
et percussit omne primogenitum in terra eorum primitias omnis laboris eorum
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
et eduxit eos in argento et auro et non erat in tribubus eorum infirmus
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
laetata est Aegyptus in profectione eorum quia incubuit timor eorum super eos
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
expandit nubem in protectionem eorum et ignem ut luceret eis per noctem
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
petierunt et venit coturnix et panem caeli saturavit eos
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
disrupit petram et fluxerunt aquae abierunt in sicco flumina
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
quoniam memor fuit verbi sancti sui quod habuit ad Abraham puerum suum
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
et eduxit populum suum in exultatione et electos suos in laetitia
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
et dedit illis regiones gentium et labores populorum possederunt
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
ut custodiant iustificationes eius et legem eius requirant

< Zabura 105 >