< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Bekennet Jehovah, rufet Seinen Namen an! Macht Seine Taten kund unter den Völkern.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Singet Ihm, singt Psalmen, sinnet nach über alle Seine Wunder.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Rühmet euch des Namens Seiner Heiligkeit; es sei fröhlich das Herz derer, die Jehovah suchen.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Nach Jehovah fragt und nach Seiner Stärke; sucht beständig Sein Angesicht.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Gedenket Seiner Wunder, die Er getan, Seiner Wahrzeichen und der Gerichte Seines Mundes.
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Ihr Samen Abrahams, Seines Knechtes, ihr Söhne Jakobs, Seine Auserwählten.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Er, Jehovah, ist unser Gott; auf der ganzen Erde sind Seine Gerichte.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
In Ewigkeit gedenkt Er Seines Bundes, des Wortes, das Er geboten, für tausend Geschlechter.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Den Er mit Abraham geschlossen, und Seines Schwures an Isaak.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Und Er ließ ihn erstehen für Jakob zur Satzung, für Israel zu ewigem Bunde.
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Und sprach: Dir will Ich geben das Land Kanaan zur Schnur deines Erbes.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Als sie noch Leute gering an Zahl waren, nur wenige, und Fremdlinge darinnen,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Von Völkerschaft zu Völkerschaft zogen sie, von einem Königreich zu einem anderen Volk.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Er ließ keinen Menschen sie niederdrücken, und rügte Könige um sie.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Rührt nicht an Meine Gesalbten und tut Meinen Propheten nichts Böses.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Er rief den Hunger über das Land, Er brach jeglichen Stab des Brotes.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Er sandte ihnen einen Mann voraus; zum Knechte ward Joseph verkauft.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
In Fußschellen zwangen sie seinen Fuß; in Eisen kam seine Seele,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Bis zur Zeit, daß Sein Wort kam, Jehovahs Rede ihn läuterte.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Der König sandte und ließ ihn los, der Herrscher der Völker, und tat ihm auf,
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Er setzte ihn zum Herrn für sein Haus und zum Herrscher über all sein Besitztum.
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Damit er nach seinem Willen binde seine Obersten, und weise mache seine Ältesten.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Und Israel kam nach Ägypten, und Jakob hielt sich auf als Fremdling im Lande Chams.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Und Er machte Sein Volk sehr fruchtbar und zahlreicher, denn seine Dränger waren.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Und Er verwandelte ihr Herz, Sein Volk zu hassen und wider Seine Knechte trüglich zu handeln.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Er sandte Mose, Seinen Knecht, und Aharon, den Er auserwählt hatte.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Sie taten unter ihnen Seiner Zeichen Worte und Wahrzeichen im Lande Cham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Er sandte Finsternis und es ward finster; und sie widersetzten sich Seinen Worten nicht.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Er verwandelte in Blut ihre Wasser und ließ ihre Fische sterben.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Von Fröschen wimmelte ihr Land, in den Kammern ihrer Könige.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Er sprach es und es kam der Arob, die Läuse in all ihrer Grenze.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Ihre Platzregen machte Er zu Hagel, des Feuers Flammen in ihrem Land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Und ihren Weinstock schlug Er und ihren Feigenbaum, und brach den Baum an ihrer Grenze.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Er sprach es und es kam die Heuschrecke und Grille sonder Zahl.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Und alles Kraut in ihrem Lande fraß sie, und fraß die Frucht ihres Bodens.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Und Er schlug alle Erstgeburt in ihrem Lande, die Erstlinge all ihrer Vollkraft.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Und mit Silber und Gold brachte Er sie aus. Und keiner strauchelte in seinen Stämmen.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Ägypten ward fröhlich über ihren Auszug; denn Schauer vor ihnen war auf sie gefallen.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Er breitete als Decke aus die Wolke, und Feuer, ihnen zu leuchten des Nachts.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Er erbat sich es und Er ließ Wachteln kommen, und Er sättigte sie mit dem Brote der Himmel.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Er tat den Felsen auf und es flossen Wasser, ein Fluß lief durch die Dürre.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Denn Er gedachte des Wortes Seiner Heiligkeit an Abraham, Seinen Knecht.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Und in Freuden führte Er Sein Volk aus, mit Lobpreisungen Seine Auserwählten.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Und Er gab ihnen der Völkerschaften Lande, und die Mühsal der Volksstämme nahmen sie ein.
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Auf daß sie hielten Seine Satzungen und bewahrten Seine Gesetze. Hallelujah!

< Zabura 105 >