< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Danket dem HERRN und predigt seinen Namen; verkündigt sein Tun unter den Völkern!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Singet von ihm und lobet ihn; redet von allen seinen Wundern!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Rühmet seinen heiligen Namen; es freue sich das Herz derer, die den HERRN suchen!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Fraget nach dem HERRN und nach seiner Macht, suchet sein Antlitz allewege!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Gedenket seiner Wunderwerke, die er getan hat, seiner Wunder und der Gerichte seines Mundes,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
ihr, der Same Abrahams, seines Knechtes, ihr Kinder Jakobs, seine Auserwählten!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Er ist der HERR, unser Gott; er richtet in aller Welt.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Er gedenkt ewiglich an seinen Bund, des Wortes, das er verheißen hat auf tausend Geschlechter,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
den er gemacht hat mit Abraham, und des Eides mit Isaak;
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
und stellte es Jakob zu einem Rechte und Israel zum ewigen Bunde
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
und sprach: “Dir will ich das Land Kanaan geben, das Los eures Erbes,”
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
da sie wenig und gering waren und Fremdlinge darin.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Und sie zogen von Volk zu Volk, von einem Königreich zum andern Volk.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Er ließ keinen Menschen ihnen Schaden tun und strafte Könige um ihretwillen.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
“Tastet meine Gesalbten nicht an und tut meinen Propheten kein Leid!”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Und er ließ Teuerung ins Land kommen und entzog allen Vorrat des Brots.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Er sandte einen Mann vor ihnen hin; Joseph ward zum Knecht verkauft.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Sie zwangen seine Füße in den Stock, sein Leib mußte in Eisen liegen,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
bis daß sein Wort kam und die Rede des HERRN ihn durchläuterte.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Da sandte der König hin und ließ ihn losgeben; der HERR über Völker hieß ihn herauslassen.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Er setzte ihn zum Herrn über sein Haus, zum Herrscher über alle seine Güter,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
daß er seine Fürsten unterwiese nach seiner Weise und seine Ältesten Weisheit lehrte.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Und Israel zog nach Ägypten, und Jakob ward ein Fremdling im Lande Hams.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Und er ließ sein Volk sehr wachsen und machte sie mächtiger denn ihre Feinde.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Er verkehrte jener Herz, daß sie seinem Volk gram wurden und dachten, seine Knechte mit List zu dämpfen.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Er sandte seinen Knecht Mose, Aaron, den er erwählt hatte.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Dieselben taten seine Zeichen unter ihnen und seine Wunder im Lande Hams.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Er ließ Finsternis kommen und machte es finster; und sie waren nicht ungehorsam seinen Worten.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Er verwandelte ihre Wasser in Blut und tötete ihre Fische.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Ihr Land wimmelte Frösche heraus in den Kammern ihrer Könige.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Er sprach: da kam Ungeziefer, Stechmücken in all ihr Gebiet.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Er gab ihnen Hagel zum Regen, Feuerflammen in ihrem Lande
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
und schlug ihre Weinstöcke und Feigenbäume und zerbrach die Bäume in ihrem Gebiet.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Er sprach: da kamen Heuschrecken und Käfer ohne Zahl.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Und sie fraßen alles Gras in ihrem Lande und fraßen die Früchte auf ihrem Felde.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Er schlug alle Erstgeburt in Ägypten, alle Erstlinge ihrer Kraft.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Und er führte sie aus mit Silber und Gold; und war kein Gebrechlicher unter ihren Stämmen.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Ägypten ward froh, daß sie auszogen; denn ihre Furcht war auf sie gefallen.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Er breitete eine Wolke aus zur Decke und ein Feuer, des Nachts zu leuchten.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Sie baten: da ließ er Wachteln kommen; und er sättigte sie mit Himmelsbrot.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Er öffnete den Felsen: da floß Wasser heraus, daß Bäche liefen in der dürren Wüste.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Denn er gedachte an sein heiliges Wort, das er Abraham, seinem Knecht, hatte geredet.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Also führte er sein Volk in Freuden und seine Auserwählten in Wonne
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
und gab ihnen die Länder der Heiden, daß sie die Güter der Völker einnahmen,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
auf daß sie halten sollten seine Rechte und sein Gesetze bewahren. Halleluja!