< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Danket dem HERRN und prediget seinen Namen; verkündiget sein Tun unter den Völkern;
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
singet von ihm und lobet ihn; redet von allen seinen Wundern;
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
rühmet seinen heiligen Namen; es freue sich das Herz derer, die den HERRN suchen!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Fraget nach dem HERRN und nach seiner Macht; suchet sein Antlitz allewege!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Gedenket seiner Wunderwerke, die er getan hat, seiner Wunder und seines Worts,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
ihr, der Same Abrahams, seines Knechts, ihr Kinder Jakobs, seine Auserwählten!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Er ist der HERR, unser Gott; er richtet in aller Welt.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Er gedenket ewiglich an seinen Bund, des Worts, das er verheißen hat auf viel tausend für und für
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
den er gemacht hat mit Abraham, und des Eides mit Isaak,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
und stellete dasselbige Jakob zu einem Recht und Israel zum ewigen Bunde
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
und sprach: Dir will ich das Land Kanaan geben, das Los eures Erbes,
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
da sie wenig und geringe waren und Fremdlinge drinnen.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Und sie zogen von Volk zu Volk, von einem Königreiche zum andern Volk.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Er ließ keinen Menschen ihnen Schaden tun und strafte Könige um ihretwillen.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Tastet meine Gesalbten nicht an und tut meinen Propheten kein Leid!
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Und er ließ eine Teurung ins Land kommen und entzog allen Vorrat des Brots.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Er sandte einen Mann vor ihnen hin; Joseph ward zum Knechte verkauft.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Sie zwangen seine Füße im Stock, sein Leib mußte in Eisen liegen,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
bis daß sein Wort kam und die Rede des HERRN ihn durchläuterte.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Da sandte der König hin und ließ ihn losgeben, der HERR über Völker hieß ihn auslassen.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Er setzte ihn zum HERRN über sein Haus, zum HERRSCher über alle seine Güter,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
daß er seine Fürsten unterweisete nach seiner Weise und seine Ältesten Weisheit lehrete.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Und Israel zog nach Ägypten, und Jakob ward ein Fremdling im Lande Hams.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Und er ließ sein Volk sehr wachsen und machte sie mächtiger denn ihre Feinde.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Er verkehrete jener Herz, daß sie seinem Volk gram wurden und dachten seine Knechte mit List zu dämpfen.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Er sandte seinen Knecht Mose, Aaron, den er hatte erwählet.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Dieselben taten seine Zeichen unter ihnen und seine Wunder im Lande Hams.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Er ließ Finsternis kommen und machte es finster; und waren nicht ungehorsam seinen Worten.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Er verwandelte ihre Wasser in Blut und tötete ihre Fische.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Ihr Land wimmelte Kröten heraus in den Kammern ihrer Könige.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Er sprach, da kam Ungeziefer, Läuse, in allen ihren Grenzen.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Er gab ihnen Hagel zum Regen, Feuerflammen in ihrem Lande;
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
und schlug ihre Weinstöcke und Feigenbäume und zerbrach die Bäume in ihren Grenzen.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Er sprach, da kamen Heuschrecken und Käfer ohne Zahl.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Und sie fraßen alles Gras in ihrem Lande und fraßen die Früchte auf ihrem Felde.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Und schlug alle Erstgeburt in Ägypten, alle ihre ersten Erben.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Und führete sie aus mit Silber und Golde; und war kein Gebrechlicher unter ihren Stämmen.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Ägypten ward froh, daß sie auszogen; denn ihre Furcht war auf sie gefallen.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Er breitete eine Wolke aus zur Decke und ein Feuer des Nachts zu leuchten.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Sie baten, da ließ er Wachteln kommen; und er sättigte sie mit Himmelbrot.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Er öffnete den Felsen, da flossen Wasser aus, daß Bäche liefen in der dürren Wüste.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Denn er gedachte an sein heiliges Wort, Abraham, seinem Knechte, geredet.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Also führete er sein Volk aus mit Freuden und seine Auserwählten mit Wonne
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
und gab ihnen die Länder der Heiden, daß sie die Güter der Völker einnahmen
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
auf daß sie halten sollten seine Rechte und seine Gesetze bewahren. Halleluja!

< Zabura 105 >