< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Célébrez l'Éternel; invoquez son nom; faites connaître parmi les peuples ses hauts faits!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Chantez-lui, psalmodiez-lui; parlez de toutes ses merveilles!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glorifiez-vous de son saint nom; que le cœur de ceux qui cherchent l'Éternel se réjouisse!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Recherchez l'Éternel et sa force; cherchez continuellement sa face!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Souvenez-vous des merveilles qu'il a faites, de ses miracles et des jugements de sa bouche;
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Vous, postérité d'Abraham, son serviteur, enfants de Jacob, ses élus!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
C'est lui, l'Éternel, qui est notre Dieu; ses jugements sont sur toute la terre.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Il se souvient à jamais de son alliance, de sa promesse établie pour mille générations;
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Du traité qu'il fit avec Abraham, et du serment qu'il fit à Isaac,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Et qu'il a confirmé à Jacob pour être un statut, à Israël pour être une alliance éternelle,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Disant: Je te donnerai le pays de Canaan; c'est le lot de votre héritage;
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Lorsqu'ils n'étaient qu'une poignée de gens, peu nombreux et étrangers dans le pays,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Allant de nation en nation, et d'un royaume vers un autre royaume.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Il ne permit à personne de les opprimer, et il châtia des rois à cause d'eux,
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Disant: Ne touchez pas à mes oints, et ne faites point de mal à mes prophètes!
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Il appela sur la terre la famine, et rompit tout l'appui du pain.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
II envoya devant eux un homme; Joseph fut vendu comme esclave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
On lui serra les pieds dans des ceps, et sa vie fut mise dans les fers;
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Jusqu'au temps où ce qu'il avait dit arriva, où la parole de l'Éternel le fit connaître.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Le roi l'envoya délivrer; le dominateur des peuples le fit élargir.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Il l'établit seigneur de sa maison, et gouverneur de tous ses biens;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Pour enchaîner à son gré ses princes, et enseigner à ses anciens la sagesse.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Alors Israël vint en Égypte; Jacob séjourna au pays de Cham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Dieu fit fort multiplier son peuple, et le rendit plus puissant que ses oppresseurs.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Puis il changea leur cœur, tellement qu'ils haïrent son peuple, et agirent perfidement contre ses serviteurs.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Il envoya Moïse, son serviteur, Aaron qu'il avait élu.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Ils opérèrent au milieu d'eux ses prodiges, et des miracles dans le pays de Cham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Il envoya des ténèbres, et produisit l'obscurité; et ils ne furent pas rebelles à sa parole.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Il changea leurs eaux en sang, et fit mourir leurs poissons.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Leur terre fourmilla de grenouilles, jusque dans les chambres de leurs rois.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Il parla, et des insectes vinrent, des moucherons dans tout leur territoire.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Il leur donna pour pluie de la grêle, des flammes de feu sur leur pays.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Il frappa leurs vignes et leurs figuiers, et brisa les arbres de leur territoire.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Il parla, et des sauterelles vinrent, des insectes rongeurs sans nombre,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Qui dévorèrent toute l'herbe de leur pays, qui dévorèrent les fruits de leurs champs.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Il frappa tous les premiers-nés dans leur pays, toutes les prémices de leur force.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Puis il les fit sortir avec de l'argent et de l'or; et dans leurs tribus il n'y eut personne qui chancelât.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
L'Égypte se réjouit à leur départ, car la frayeur d'Israël les avait saisis.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Il étendit la nuée pour les couvrir, et le feu pour les éclairer de nuit.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
A leur demande, il fit venir des cailles; et il les rassasia du pain des cieux.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Il ouvrit le rocher, et les eaux coulèrent; elles coururent, par les lieux secs, comme un fleuve.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Car il se souvenait de sa parole sainte, et d'Abraham, son serviteur.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Et il fit sortir son peuple avec allégresse, ses élus avec des chants de joie.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Il leur donna les terres des nations, et ils possédèrent le travail des peuples;
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Afin qu'ils gardassent ses ordonnances, et qu'ils observassent ses lois. Louez l'Éternel!

< Zabura 105 >