< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Louez l’Éternel, invoquez son nom! Faites connaître parmi les peuples ses hauts faits!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Chantez, chantez en son honneur! Parlez de toutes ses merveilles!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glorifiez-vous de son saint nom! Que le cœur de ceux qui cherchent l’Éternel se réjouisse!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Ayez recours à l’Éternel et à son appui, Cherchez continuellement sa face!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Souvenez-vous des prodiges qu’il a faits, De ses miracles et des jugements de sa bouche,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Postérité d’Abraham, son serviteur, Enfants de Jacob, ses élus!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
L’Éternel est notre Dieu; Ses jugements s’exercent sur toute la terre.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Il se rappelle à toujours son alliance, Ses promesses pour mille générations,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
L’alliance qu’il a traitée avec Abraham, Et le serment qu’il a fait à Isaac;
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Il l’a érigée pour Jacob en loi, Pour Israël en alliance éternelle,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Disant: Je te donnerai le pays de Canaan Comme héritage qui vous est échu.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Ils étaient alors peu nombreux, Très peu nombreux, et étrangers dans le pays,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Et ils allaient d’une nation à l’autre Et d’un royaume vers un autre peuple;
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Mais il ne permit à personne de les opprimer, Et il châtia des rois à cause d’eux:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Ne touchez pas à mes oints, Et ne faites pas de mal à mes prophètes!
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Il appela sur le pays la famine, Il coupa tout moyen de subsistance.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Il envoya devant eux un homme: Joseph fut vendu comme esclave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
On serra ses pieds dans des liens, On le mit aux fers,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Jusqu’au temps où arriva ce qu’il avait annoncé, Et où la parole de l’Éternel l’éprouva.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Le roi fit ôter ses liens, Le dominateur des peuples le délivra.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Il l’établit seigneur sur sa maison, Et gouverneur de tous ses biens,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Afin qu’il pût à son gré enchaîner ses princes, Et qu’il enseignât la sagesse à ses anciens.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Alors Israël vint en Égypte, Et Jacob séjourna dans le pays de Cham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Il rendit son peuple très fécond, Et plus puissant que ses adversaires.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Il changea leur cœur, au point qu’ils haïrent son peuple Et qu’ils traitèrent ses serviteurs avec perfidie.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Il envoya Moïse, son serviteur, Et Aaron, qu’il avait choisi.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Ils accomplirent par son pouvoir des prodiges au milieu d’eux, Ils firent des miracles dans le pays de Cham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Il envoya des ténèbres et amena l’obscurité, Et ils ne furent pas rebelles à sa parole.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Il changea leurs eaux en sang, Et fit périr leurs poissons.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Le pays fourmilla de grenouilles, Jusque dans les chambres de leurs rois.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Il dit, et parurent les mouches venimeuses, Les poux sur tout leur territoire.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Il leur donna pour pluie de la grêle, Des flammes de feu dans leur pays.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Il frappa leurs vignes et leurs figuiers, Et brisa les arbres de leur contrée.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Il dit, et parurent les sauterelles, Des sauterelles sans nombre,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Qui dévorèrent toute l’herbe du pays, Qui dévorèrent les fruits de leurs champs.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Il frappa tous les premiers-nés dans leur pays, Toutes les prémices de leur force.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Il fit sortir son peuple avec de l’argent et de l’or, Et nul ne chancela parmi ses tribus.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Les Égyptiens se réjouirent de leur départ, Car la terreur qu’ils avaient d’eux les saisissait.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Il étendit la nuée pour les couvrir, Et le feu pour éclairer la nuit.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
A leur demande, il fit venir des cailles, Et il les rassasia du pain du ciel.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Il ouvrit le rocher, et des eaux coulèrent; Elles se répandirent comme un fleuve dans les lieux arides.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Car il se souvint de sa parole sainte, Et d’Abraham, son serviteur.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Il fit sortir son peuple dans l’allégresse, Ses élus au milieu des cris de joie.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Il leur donna les terres des nations, Et ils possédèrent le fruit du travail des peuples,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Afin qu’ils gardassent ses ordonnances, Et qu’ils observassent ses lois. Louez l’Éternel!