< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Rendez grâce à Yahvé! Invoquez son nom! Faites connaître ses actions parmi les peuples.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Chantez-lui, chantez-lui des louanges! Racontez toutes ses œuvres merveilleuses.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Gloire à son saint nom. Que le cœur de ceux qui cherchent Yahvé se réjouisse.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Recherchez Yahvé et sa force. Cherchez son visage pour toujours.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Rappelez-vous les merveilles qu'il a faites: ses merveilles, et les jugements de sa bouche,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
vous, descendants d'Abraham, son serviteur, vous, enfants de Jacob, ses élus.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Il est Yahvé, notre Dieu. Ses jugements sont dans toute la terre.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Il s'est souvenu de son alliance pour toujours, la parole qu'il a commandée à mille générations,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
l'alliance qu'il a conclue avec Abraham, son serment à Isaac,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
et l'a confirmé à Jacob pour une loi; à Israël pour une alliance éternelle,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
en disant: « Je vous donnerai le pays de Canaan, le lot de votre héritage, »
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
alors qu'ils n'étaient qu'un petit nombre d'hommes, oui, très peu, et des étrangers en son sein.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Ils allaient de nation en nation, d'un royaume à un autre peuple.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Il n'a permis à personne de leur faire du mal. Oui, il a réprimandé les rois pour leur bien,
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
« Ne touchez pas à mes oints! Ne faites pas de mal à mes prophètes! »
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Il a appelé la famine sur le pays. Il a détruit les réserves de nourriture.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Il envoya un homme devant eux. Joseph a été vendu comme esclave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
On lui a meurtri les pieds avec des entraves. Son cou a été mis aux fers,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
jusqu'au moment où sa parole s'est accomplie, et la parole de Yahvé lui a donné raison.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Le roi l'envoya et le libéra, même le chef des peuples, et le laisser libre.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Il l'a fait seigneur de sa maison, et le maître de toutes ses possessions,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
pour discipliner ses princes à son gré, et d'enseigner la sagesse à ses aînés.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Israël aussi est venu en Égypte. Jacob a vécu dans le pays de Ham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Il a beaucoup augmenté son peuple, et les a rendus plus forts que leurs adversaires.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Il a détourné leur cœur pour qu'ils haïssent son peuple, pour conspirer contre ses serviteurs.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Il envoya Moïse, son serviteur, et Aaron, qu'il avait choisi.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Ils faisaient des miracles au milieu d'eux, et des merveilles dans le pays de Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Il a envoyé les ténèbres, et il a rendu les ténèbres. Ils ne se sont pas rebellés contre ses paroles.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Il a changé leurs eaux en sang, et ont tué leurs poissons.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Leur terre grouillait de grenouilles, même dans les chambres de leurs rois.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Il parla, et des nuées de mouches vinrent, et des poux dans toutes leurs frontières.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Il leur a donné de la grêle en guise de pluie, avec des éclairs dans leur pays.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Il a frappé leurs vignes et aussi leurs figuiers, et ont brisé les arbres de leur pays.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Il parla, et les sauterelles vinrent avec les sauterelles, sans nombre.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Ils ont dévoré toutes les plantes de leur pays, et ont mangé le fruit de leur sol.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Il frappa aussi tous les premiers-nés de leur pays, les premiers fruits de toute leur virilité.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Il les fit sortir avec de l'argent et de l'or. Il n'y avait pas une seule personne faible parmi ses tribus.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
L'Égypte se réjouit de leur départ, car la peur d'eux était tombée sur eux.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Il a étendu un nuage pour le couvrir, le feu pour donner de la lumière dans la nuit.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Ils ont demandé, et il a apporté des cailles, et les a rassasiés avec le pain du ciel.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Il ouvrit le rocher, et des eaux jaillirent. Ils coulaient comme un fleuve dans les endroits secs.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Car il s'est souvenu de sa sainte parole, et Abraham, son serviteur.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Il a fait sortir son peuple avec joie, son choix avec le chant.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Il leur a donné les terres des nations. Ils ont pris le travail des peuples en possession,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
afin qu'ils gardent ses statuts, et observez ses lois. Louez Yah!

< Zabura 105 >