< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Alleluya. Knouleche ye to the Lord, and inwardli clepe ye his name; telle ye hise werkis among hethen men.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Synge ye to hym, and seie ye salm to him, and telle ye alle hise merueylis;
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
be ye preisid in his hooli name. The herte of men sekynge the Lord be glad;
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
seke ye the Lord, and be ye confermed; seke ye euere his face.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Haue ye mynde on hise merueilis, whiche he dide; on his grete wondris, and domes of his mouth.
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
The seed of Abraham, his seruaunt; the sones of Jacob, his chosun man.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He is oure Lord God; hise domes ben in al the erthe.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He was myndeful of his testament in to the world; of the word which he comaundide in to a thousynde generaciouns.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Which he disposide to Abraham; and of his ooth to Isaac.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
And he ordeynede it to Jacob in to a comaundement; and to Israel in to euerlastinge testament.
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
And he seide, I shal yiue to thee the lond of Canaan; the cord of youre eritage.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Whanne thei weren in a litil noumbre; and the comelingis of hem weren ful fewe.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
And thei passiden fro folk in to folk; and fro a rewme in to another puple.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
He lefte not a man to anoye hem; and he chastiside kyngis for hem.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Nile ye touche my cristis; and nyle ye do wickidli among my prophetis.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
And God clepide hungir on erthe; and he wastide al the stidefastnesse of breed.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
He sente a man bifore hem; Joseph was seeld in to a seruaunt.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Thei maden lowe hise feet in stockis, irun passide by his soule; til the word of him cam.
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
The speche of the Lord enflawmede him;
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
the king sente and vnbond hym; the prince of puplis sente and delyuerede him.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He ordeynede him the lord of his hous; and the prince of al his possessioun.
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
That he schulde lerne hise princis as him silf; and that he schulde teche hise elde men prudence.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
And Israel entride in to Egipt; and Jacob was a comeling in the lond of Cham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
And God encreesside his puple greetli; and made hym stidefast on hise enemyes.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turnede the herte of hem, that thei hatiden his puple; and diden gile ayens hise seruauntis.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
He sent Moises, his seruaunt; thilke Aaron, whom he chees.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
He puttide in hem the wordis of hise myraclis; and of hise grete wondris in the lond of Cham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He sente derknessis, and made derk; and he made not bitter hise wordis.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turnede the watris of hem in to blood; and he killide the fischis of hem.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
And the lond of hem yaf paddoks; in the priue places of the kyngis of hem.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
God seide, and a fleische flie cam; and gnattis in alle the coostis of hem.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He settide her reynes hail; fier brennynge in the lond of hem.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
And he smoot the vynes of hem, and the fige trees of hem; and al to-brak the tree of the coostis of hem.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He seide, and a locuste cam; and a bruk of which was noon noumbre.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
And it eet al the hey in the lond of hem; and it eet al the fruyt of the lond of hem.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
And he killide ech the firste gendrid thing in the lond of hem; the firste fruitis of alle the trauel of hem.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
And he ledde out hem with siluer and gold; and noon was sijk in the lynagis of hem.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egipt was glad in the goyng forth of hem; for the drede of hem lai on Egipcians.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spredde abrood a cloude, in to the hiling of hem; and fier, that it schynede to hem bi nyyt.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Thei axiden, and a curlew cam; and he fillide hem with the breed of heuene.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He brak a stoon, and watris flowiden; floodis yeden forth in the drye place.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For he was myndeful of his hooli word; which he hadde to Abraham, his child.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
And he ledde out his puple in ful out ioiyng; and hise chosun men in gladnesse.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
And he yaf to hem the cuntreis of hethen men; and thei hadden in possessioun the trauels of puplis.
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
That thei kepe hise iustifiyngis; and seke his lawe.