< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
O give thanks unto the LORD; Call upon his name; Make known his deeds among the people!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing unto him; sing psalms unto him; Tell ye of all his wondrous works!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glory ye in his holy name; Let the hearts of them that seek the LORD rejoice!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek the LORD, and his majesty; Seek his face continually!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember the wonders he hath wrought, His miracles and the judgments of his mouth,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Ye offspring of Abraham his servant, Ye children of Jacob his chosen!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Jehovah, he is our God, His judgments are over all the earth.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He remembereth his covenant for ever, And the promise to a thousand generations;
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
The covenant which he made with Abraham, And the oath which he gave to Isaac;
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Which he confirmed to Jacob for a decree, And to Israel for an everlasting covenant.
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
“To thee,” said he, “will I give the land of Canaan For the lot of your inheritance.”
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
When they were yet few in number, Very few, and strangers in the land;
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
When they went from nation to nation, From one kingdom to another people,
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
He suffered no man to oppress them; Yea, he rebuked kings for their sakes.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
“Touch not,” said he, “mine anointed, And do my prophets no harm!”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Again, when he commanded a famine in the land, And broke the whole staff of bread,
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
He sent a man before them; Joseph was sold as a slave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
His feet they hurt with fetters; He was bound in chains of iron;
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Until his prediction came to pass, And the word of the LORD proved him.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Then the king sent, and loosed him; The ruler of nations, and set him free;
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He made him governor of his house, And lord of all his possessions;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
To bind his princes at his pleasure, And teach his counsellors wisdom.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Israel also came into Egypt, And Jacob sojourned in the land of Ham;
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Where God increased his people greatly, And made them stronger than their enemies.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turned their hearts to hate his people, And form devices against his servants.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Then sent he Moses his servant, And Aaron, whom he had chosen.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
They showed his signs among them, And his wonders in the land of Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He sent darkness upon them, and made it dark; And they did not disobey his word.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turned their waters into blood, And caused their fish to die.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land brought forth frogs in abundance, Even in the chambers of their kings.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
He spake, and there came flies, And lice in all their coasts.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Instead of rain he gave them hail, And flaming fire in their land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
He smote also their vines and fig-trees, And broke the trees of their coasts.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He spake, and the locusts came. Destructive locusts without number,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Which ate up all the herbage in their land, And devoured the fruits of their fields.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Then he smote all the first-born in their land, The first-fruits of all their strength.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
He led forth his people with silver and gold; Nor was there one feeble person in all their tribes.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt was glad when they departed, For their terror had fallen upon them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spread out a cloud for a covering, And fire to give light by night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
They asked, and he brought quails, And satisfied them with the bread of heaven.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He opened the rock, and the waters gushed forth, And ran in the dry places like a river.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For he remembered his holy promise, Which he had made to Abraham his servant;
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
And he led forth his people with joy, And his chosen with gladness.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
He gave to them the lands of the nations, And they inherited the labor of the peoples;
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
That they might observe his statutes, And obey his laws. Praise ye the LORD!