< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Give thanks to YHWH—call on His Name, Make His acts known among the peoples.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing to Him—sing praise to Him, Meditate on all His wonders.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Boast yourselves in His Holy Name, The heart of those seeking YHWH rejoices.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek YHWH and His strength, Seek His face continually.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember His wonders that He did, His signs and the judgments of His mouth.
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
O seed of Abraham, His servant, O sons of Jacob, His chosen ones.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He [is] our God YHWH, His judgments [are] in all the earth.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He has remembered His covenant for all time, The word He commanded to one thousand generations,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
That He has made with Abraham, And His oath to Isaac,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
And establishes it to Jacob for a statute, To Israel—a perpetual covenant,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Saying, “I give the land of Canaan to you, The portion of your inheritance,”
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
In their being few in number, But a few, and sojourners in it.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
And they go up and down, from nation to nation, From a kingdom to another people.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
He has not permitted any to oppress them And He reproves kings for their sakes.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
“Do not strike against My anointed, And do no evil to My prophets.”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
And He calls a famine on the land, He has broken the whole staff of bread.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
He has sent a man before them, Joseph has been sold for a servant.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
They have afflicted his feet with chains, Iron has entered his soul,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Until the time of the coming of His word The saying of YHWH has tried him.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
The king has sent, and looses him, The ruler of the peoples, and draws him out.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He has made him lord of his house, And ruler over all his possessions.
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
To bind his chiefs at his pleasure, And he makes his elderly wise.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
And Israel comes into Egypt, And Jacob has sojourned in the land of Ham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
And He makes His people very fruitful, And makes it mightier than its adversaries.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turned their heart to hate His people, To conspire against His servants.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
He has sent His servant Moses, Aaron whom He had fixed on.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
They have set among them the matters of His signs, And wonders in the land of Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He has sent darkness, and it is dark, And they have not provoked His word.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He has turned their waters to blood, And puts their fish to death.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land has teemed [with] frogs, In the inner chambers of their kings.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
He has commanded, and the beetle comes, Lice into all their border.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He has made their showers hail, A flaming fire [is] in their land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
And He strikes their vine and their fig, And shatters the trees of their border.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He has commanded, and the locust comes, And the cankerworm—innumerable,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
And it consumes every herb in their land, And it consumes the fruit of their ground.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
And He strikes every firstborn in their land, The first-fruit of all their strength,
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
And brings them out with silver and gold, And there is not a feeble one in its tribes.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt has rejoiced in their going forth, For their fear had fallen on them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He has spread a cloud for a covering, And fire to enlighten the night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
They have asked, and He brings quails, And satisfies them [with] bread of the heavens.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He has opened a rock, and waters flow, They have gone on in dry places—a river.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For He has remembered His holy word, With His servant Abraham,
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
And He brings forth His people with joy, His chosen ones with singing.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
And He gives to them the lands of nations, And they possess the labor of peoples,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
That they may observe His statutes, And may keep His laws. Praise YAH!