< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Praise the Lord, and call vpon his Name: declare his workes among the people.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing vnto him, sing prayse vnto him, and talke of all his wonderous workes.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Reioyce in his holy Name: let the heart of them that seeke the Lord, reioyce.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seeke the Lord and his strength: seeke his face continually.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember his marueilous woorkes, that he hath done, his wonders and the iudgements of his mouth,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Ye seede of Abraham his seruant, ye children of Iaakob, which are his elect.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He is the Lord our God: his iudgements are through all the earth.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He hath alway remembred his couenant and promise, that he made to a thousand generations,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Euen that which he made with Abraham, and his othe vnto Izhak:
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
And since hath confirmed it to Iaakob for a lawe, and to Israel for an euerlasting couenant,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Saying, Vnto thee will I giue the land of Canaan, the lot of your inheritance.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Albeit they were fewe in nomber, yea, very fewe, and strangers in the land,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
And walked about from nation to nation, from one kingdome to another people,
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Yet suffered he no man to doe them wrong, but reprooued Kings for their sakes, saying,
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Touche not mine anointed, and doe my Prophets no harme.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Moreouer, he called a famine vpon ye land, and vtterly brake the staffe of bread.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
But he sent a man before them: Ioseph was solde for a slaue.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
They helde his feete in the stockes, and he was laide in yrons,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Vntill his appointed time came, and the counsell of the Lord had tryed him.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
The King sent and loosed him: euen the Ruler of the people deliuered him.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He made him lord of his house, and ruler of all his substance,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
That he shoulde binde his princes vnto his will, and teach his Ancients wisedome.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Then Israel came to Egypt, and Iaakob was a stranger in the land of Ham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
And he increased his people exceedingly, and made them stronger then their oppressours.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turned their heart to hate his people, and to deale craftily with his seruants.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Then sent he Moses his seruant, and Aaron whom he had chosen.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
They shewed among them the message of his signes, and wonders in the land of Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He sent darkenesse, and made it darke: and they were not disobedient vnto his commission.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turned their waters into blood, and slewe their fish.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land brought foorth frogs, euen in their Kings chambers.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
He spake, and there came swarmes of flies and lice in all their quarters.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He gaue them haile for raine, and flames of fire in their land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
He smote their vines also and their figge trees, and brake downe the trees in their coastes.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He spake, and the grashoppers came, and caterpillers innumerable,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
And did eate vp all the grasse in their land, and deuoured the fruite of their ground.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
He smote also all the first borne in their land, euen the beginning of all their strength.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
He brought them forth also with siluer and golde, and there was none feeble among their tribes.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt was glad at their departing: for the feare of them had fallen vpon them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spred a cloude to be a couering, and fire to giue light in the night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
They asked, and he brought quailes, and he filled them with the bread of heauen.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He opened the rocke, and the waters flowed out, and ranne in the drye places like a riuer.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For he remembred his holy promise to Abraham his seruant,
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
And he brought forth his people with ioy, and his chosen with gladnesse,
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
And gaue them the lands of the heathen, and they tooke the labours of the people in possession,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
That they might keepe his statutes, and obserue his Lawes. Prayse ye the Lord.

< Zabura 105 >