< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Alleluia. Give glory to the Lord, and call upon his name: declare his deeds among the Gentiles.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing to him, yea sing praises to him: relate all his wondrous works.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glory ye in his holy name: let the heart of them rejoice that seek the Lord.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek ye the Lord, and be strengthened: seek his face evermore.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember his marvellous works which he hath done; his wonders, and the judgments of his mouth.
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
O ye seed of Abraham his servant; ye sons of Jacob his chosen.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He is the Lord our God: his judgments are in all the earth.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He hath remembered his covenant for ever: the word which he commanded to a thousand generations.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Which he made to Abraham; and his oath to Isaac:
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
And he appointed the same to Jacob for a law, and to Israel for an everlasting testament:
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Saying: To thee will I give the land of Chanaan, the lot of your inheritance.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
When they were but a small number: yea very few, and sojourners therein:
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
And they passed from nation to nation, and from one kingdom to another people.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
He suffered no man to hurt them: and he reproved kings for their sakes.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Touch ye not my anointed: and do no evil to my prophets.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
And he called a famine upon the land: and he broke in pieces all the support of bread.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
He sent a man before them: Joseph, who was sold for a slave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
They humbled his feet in fetters: the iron pierced his soul,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Until his word came. The word of the Lord inflamed him.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
The king sent, and he released him: the ruler of the people, and he set him at liberty.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He made him master of his house, and ruler of all his possession.
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
That he might instruct his princes as himself, and teach his ancients wisdom.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
And Israel went into Egypt: and Jacob was a sojourner in the land of Cham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
And he increased his people exceedingly: and strengthened them over their enemies,
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turned their heart to hate his people: and to deal deceitfully with his servants.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
He sent Moses his servant: Aaron the man whom he had chosen.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
He gave them power to shew his signs, and his wonders in the land of Cham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He sent darkness, and made it obscure: and grieved not his words.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turned their waters into blood, and destroyed their fish.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land brought forth frogs, in the inner chambers of their kings.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
He spoke, and there came divers sorts of flies and sciniphs in all their coasts.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He gave them hail for rain, a burning fire in the land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
And he destroyed their vineyards and their fig trees: and he broke in pieces the trees of their coasts.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He spoke, and the locust came, and the bruchus, of which there was no number.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
And they devoured all the grass in their land, and consumed all the fruit of their ground.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
And he slew all the firstborn in their land: the firstfruits of all their labour.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
And he brought them out with silver and gold: and there was not among their tribes one that was feeble.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt was glad when they departed: for the fear of them lay upon them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spread a cloud for their protection, and fire to give them light in the night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
They asked, and the quail came: and he filled them with the bread of heaven.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He opened the rock, and waters flowed: rivers ran down in the dry land.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Because he remembered his holy word, which he had spoken to his servant Abraham.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
And he brought forth his people with joy, and his chosen with gladness.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
And he gave them the lands of the Gentiles: and they possessed the labours of the people:
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
That they might observe his justifications, and seek after his law.