< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Hvalite Jahvu, prizivajte mu ime, navješćujte među narodima djela njegova!
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Pjevajte mu, svirajte mu, pripovijedajte sva njegova čudesa!
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Dičite se svetim imenom njegovim, neka se raduje srce onih što traže Jahvu!
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Tražite Jahvu i njegovu snagu, tražite svagda njegovo lice!
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Sjetite se čudesa koja učini, njegovih čuda i sudova usta njegovih!
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Abrahamov rod sluga je njegov, sinovi Jakovljevi njegovi izabranici!
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
On je Jahve, Bog naš; po svoj su zemlji njegovi sudovi!
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
On se uvijek sjeća svojega Saveza, riječi koju dade tisući naraštaja:
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Saveza koji sklopi s Abrahamom i zakletve svoje Izaku.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Ustanovi je kao zakon Jakovu, Izraelu vječni Savez,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
govoreći: “Tebi ću dati kanaansku zemlju kao dio u baštinu vašu.”
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Kad ih još bješe malo na broju, vrlo malo, i kad bjehu pridošlice u njoj,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
išli su od naroda do naroda, iz jednoga kraljevstva k drugom narodu,
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
ali ne dopusti nikom da ih tlači, kažnjavaše zbog njih kraljeve:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
“Ne dirajte u moje pomazanike, ne nanosite zla mojim prorocima!”
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
I on pozva glad na zemlju, sve zalihe uništi krušne.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Pred njima čovjeka posla: Josip u ropstvo bijaše prodan.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Sputaše uzama noge njegove, u gvožđe mu vrat staviše,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
dok se ne ispuni proroštvo njegovo, Jahvina ga riječ potvrdi.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Kralj naredi da ga driješe, narÄodÄa poglavar oslobodi njega.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Za domaćina ga stavi kući svojoj, za nadstojnika sveg imanja svoga,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
da velikaše njegove po volji uči i starce njegove mudrosti da vodi.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Tad Izrael u Egipat uđe, Jakov došljak bješe u Kamovoj zemlji.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Narod svoj umnoži veoma, učini ga jačim od dušmana.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Okrenu im srce da zamrze narod njegov, da slugama njegovim opaki budu.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Mojsija posla, slugu svoga, Arona, kog odabra.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Činjahu među njima znake njegove i čudesa u Kamovoj zemlji.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Posla tmine, i smrknu se, al' prkosiše oni riječima njegovim.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
U krv im vode prometnu i pobi ribe njihove.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Zemljom im žabe provrvješe, prodriješe i u dvore kraljevske.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Reče, i muha roj doletje i komarci u sve kraje njine.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Mjesto kiše grÓad im dade, ognjene munje po njihovoj zemlji.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Udari im lozu i smokve, polomi stabla u krajima njinim.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Reče, i skakavci dođoše i bezbrojne gusjenice s njima.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
U zemlji im proždriješe svu bilinu, proždriješe rod njihovih njiva.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Pobi sve prvorođene u njihovoj zemlji, sve prvine snage njihove.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Izvede ih sa srebrom i zlatom; u plemenima njinim bolesnih ne bješe.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Odlasku njihovu Egipat se obradova, jer ga od njih strah spopade.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Rasprostro je oblak kao pokrov i oganj da se obnoć sja.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Zamoliše, i dovede prepelice, nebeskim ih kruhom tad nahrani.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Hrid rascijepi, i provri voda, pustinjom poteče kao rijeka.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Tad se sjeti svete riječi svoje što je zada sluzi svome Abrahamu.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Puk svoj s klicanjem izvede i s veseljem izabrane svoje.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
I dade im zemlje poganske, trud naroda baštiniše,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
da čuvaju naredbe njegove i zakone da mu paze. Aleluja!

< Zabura 105 >