< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Благослови, душе моя, Господа! Господи, Боже мій, Ти ве́льми великий, зодягну́вся Ти в ве́лич та в славу!
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Зодягає Він світло, як ша́ти, небеса́ простягає, немов би заві́су.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Він ставить на во́дах пала́ти Свої, хма́ри кладе за Свої колесни́ці, ходить на кри́лах вітро́вих!
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Він чинить вітри́ за Своїх посланці́в, палю́чий огонь — за Своїх слуг.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Землю Ти вгрунтува́в на осно́вах її, щоб на вічні віки вона не захита́лась,
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
безо́днею вкрив Ти її, немов шатою. Стала вода над гора́ми, —
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
від погро́зи Твоєї вона втекла́, від гу́ркоту грому Твого побігла вона, —
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
виходить на го́ри та схо́дить в доли́ни, на місце, що Ти встанови́в був для неї.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Ти границю поклав, щоб її вона не перейшла́, щоб вона не верну́лася землю покрити.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Він джере́ла пускає в пото́ки, що пливуть між гора́ми,
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
напува́ють вони всю пільну́ звірину́, ними дикі осли́ гасять спра́гу свою.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Птаство небесне над ними живе, видає воно голос з-посе́ред галу́зок.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Він напоює горн з пала́ців Своїх, із плоду чи́нів Твоїх земля си́титься.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Траву для худоби виро́щує, та зелени́ну для праці люди́ні, щоб хліб добува́ти з землі,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
і вино, що серце люди́ні воно звеселя́є, щоб більш від оливи блищало обличчя, і хліб, що серце люди́ні зміцня́є.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Насичуються Господні дере́ва, ті ке́дри лива́нські, що Ти насади́в,
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
що там ку́бляться пта́хи, бузько́, — кипари́си мешка́ння його.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Го́ри високі — для диких кози́ць, скелі — схо́вище ске́льним звіри́нам.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
і місяця Він учинив для озна́чення ча́су, сонце знає свій за́хід.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Темноту́ Ти наво́диш — і ніч настає, в ній пору́шується вся звіри́на лісна́, —
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
рича́ть левчуки́ за здоби́чею та шукають від Бога своєї пожи́ви.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Сонце ж засвітить — вони повтікають, та й кладуться по но́рах своїх.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Люди́на виходить на працю свою, й на роботу свою аж до ве́чора.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Які то числе́нні діла Твої, Господи, — Ти мудро вчинив їх усіх, Твого тво́рива повна земля!
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Ось море велике й розло́го-широ́ке, — там повзю́че, й числа їм немає, звіри́на мала́ та велика!
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Ходять там кораблі, там той левіята́н, якого створив Ти, щоб ба́витися йому в мо́рі.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Вони всі чекають Тебе, — щоб Ти ча́су свого поживу їм дав.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Даєш їм — збирають вони, руку Свою розкрива́єш — добром насича́ються.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Ховаєш обличчя Своє — то вони переля́кані, забираєш їм духа — вмирають вони, та й верта́ються до свого по́роху.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Посилаєш Ти духа Свого — вони тво́ряться, і Ти відновля́єш обличчя землі.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Нехай буде слава Господня навіки, хай діла́ми Своїми радіє Господь!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Він погляне на землю — й вона затремти́ть, доторкне́ться до гір — і диму́юти вони!
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Я буду співати Господе́ві в своє́му житті, буду грати для Бога мого, аж поки живу́!
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Буде приємна Йому моя мова, — я Господом буду радіти!
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Неха́й згинуть грі́шні з землі, а безбожні — немає вже їх! Благослови, душе моя, Господа! Алілу́я!

< Zabura 104 >