< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Lofva Herran, min själ; Herre, min Gud, du äst ganska härlig, du äst dägelig och allstinges väl beprydd.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Ljus är din klädnad, som du uppå hafver; du utsträcker himmelen såsom ett tapet.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Du hvälfver honom ofvan med vatten; du far i skyn såsom i en vagn, och går på vädrens vingar;
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Du, som gör dina Änglar till väder, och dina tjenare till eldslåga;
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Du, som grundar jordena på hennes botten, så att hon blifver i evig tid.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Med djupet betäcker du henne, såsom med ett kläde, och vatten stå öfver bergen.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Men för ditt näpsande fly de; för ditt dundrande fara de bort.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Bergen resa högt upp, och dalarna sätta sig ned i det rum, som du dem skickat hafver.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Du hafver satt ett mål, der komma de intet öfver; och måga icke åter betäcka jordena.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Du låter källor uppbrista i dalomen, så att vatten emellan bergen flyta;
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Att all djur på markene måga dricka, och vildåsnarna sin törst släcka.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
När dem sitta himmelens foglar, och sjunga på qvistarna.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Du fuktar bergen ofvanefter; du gör landet fullt med frukt, den du förskaffar.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Du låter gräs växa för boskapen, och säd menniskomen till nytto; att du skall låta komma bröd utaf jordene;
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Och att vin skall fröjda menniskones hjerta, och hennes ansigte dägeligit varda af oljo, och bröd styrka menniskones hjerta;
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Att Herrans trä skola full med must stå; de cedreträ på Libanon, som han planterat hafver.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Der hafva foglarna sitt näste, och hägrar bo uppe i furoträn.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
De höga berg äro de stengetters tillflykt, och stenklyfterna de kunilers.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Du gör månan, till att derefter skifta året; solen vet sin nedergång.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Du gör mörker, att natt varder; då draga sig all vilddjur ut;
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
De unga lejon, som ryta efter rof, och sin mat söka af Gudi;
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Men när solen uppgår, draga de bort, och lägga sig uti sina kulor.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Så går då menniskan ut till sitt arbete, och till sitt åkerverk intill aftonen.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Herre, huru äro din verk så stor och mång! Du hafver visliga skickat dem all, och jorden är full af dina ägodelar.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Hafvet, det så stort och vidt är, der kräla uti, utan tal, både stor och liten djur.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Der gå skepp; der äro hvalfiskar, som du gjort hafver, att de deruti leka skola.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Allt vänter efter dig, att du skall gifva dem mat i sin tid.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Då du gifver dem, så samla de; när du upplåter dina hand, så varda de med god ting mättade.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Om du fördöljer ditt ansigte, så varda de förskräckte; du tager deras anda bort, så förgås de, och varda åter till stoft igen.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Du låter ut din anda, så varda de skapade, och du förnyar jordenes ansigte.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Herrans ära är evig; Herren hafver behag till sin verk.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Han ser uppå jordena, så bäfvar hon; han kommer vid bergen, så ryka de.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Jag vill sjunga Herranom i mina lifsdagar, och lofva min Gud, så länge jag är till.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Mitt tal behage honom väl; jag gläder mig af Herranom.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Syndarena hafve en ända på jordene, och de ogudaktige vare icke mer till; lofva, min själ, Herran. Halleluja.

< Zabura 104 >