< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Bendice, alma mía, a Jehová; Jehová Dios mío, mucho te has engrandecido, de gloria y de hermosura te has vestido.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Que se cubre de luz como de vestidura, que extiende los cielos como una cortina;
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Que entabla con las aguas sus doblados, el que pone a las nubes por su carro, el que anda sobre las alas del viento.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
El que hace a sus ángeles espíritus, sus ministros al fuego flameante.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
El fundó la tierra sobre sus basas, no se moverá por ningún siglo.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Con el abismo, como con vestido, la cubriste: sobre los montes estaban las aguas.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
De tu reprensión huyeron; por el sonido de tu trueno se apresuraron.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Subieron los montes, descendieron los valles a este lugar, que tú les fundaste.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Pusíste les término, el cual no traspasarán, ni volverán a cubrir la tierra.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
El que envía las fuentes en los arroyos; entre los montes van.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Abrévanse todas las bestias del campo; los asnos salvajes quebrantan su sed.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Junto a ellos habitan las aves de los cielos; entre las hojas dan voces.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
El que riega los montes desde sus doblados; del fruto de tus obras se harta la tierra.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
El que hace producir el heno para las bestias; y la yerba para servicio del hombre, sacando el pan de la tierra,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Y el vino que alegra el corazón del hombre; haciendo relumbrar la faz con el aceite; y el pan sustenta el corazón del hombre.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Hártanse los árboles de Jehová; los cedros del Líbano que él plantó:
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Para que aniden allí las aves; la cigüeña tenga su casa en las hayas.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Los montes altos para las cabras monteses, las peñas madrigueras para los conejos.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Hizo la luna para sazones: el sol conoció su occidente.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Pones las tinieblas, y la noche es; en ella corren todas las bestias del monte.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Los leoncillos braman a la presa, y para buscar de Dios su comida.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Sale el sol, recógense, y échanse en sus cuevas.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Sale el hombre a su hacienda, y a su labranza hasta la tarde.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
¡Cuán muchas son tus obras, o! Jehová! todas ellas hiciste con sabiduría: la tierra está llena de tu posesión.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Esta gran mar y ancha de términos; allí hay pescados sin número, bestias pequeñas y grandes.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Allí andan navíos, este leviatán que hiciste para que jugase en ella.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Todas ellas esperan a ti, para que les des su comida a su tiempo.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Dásles, recogen: abres tu mano, hártanse de bien.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Escondes tu rostro, túrbanse: les quitas el espíritu, dejan de ser, y tórnanse en su polvo.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Envías tu espíritu, críanse: y renuevas la haz de la tierra.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Sea la gloria a Jehová para siempre: alégrese Jehová en sus obras.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
El que mira a la tierra, y tiembla: toca en los montes, y humean.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
A Jehová cantaré en mi vida: a mi Dios diré salmos mientras viviere.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Serme ha suave hablar de él: yo me alegraré en Jehová.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Sean consumidos de la tierra los pecadores: y los impíos dejen de ser. Bendice alma mía a Jehová. Alelu- Jah.