< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Teici To Kungu, mana dvēsele! Kungs, mans Dievs, Tu esi ļoti liels, ar augstību un godību aptērpies.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Tu ģērbies gaišumā kā apģērbā; tu izklāj debesis kā telti.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Tu ūdeņus augstībā sev lieci par grīdu, tu dari padebešus par saviem ratiem, tu staigā uz vēja spārniem.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Tu dari vējus par Saviem eņģeļiem un uguns liesmas par Saviem sulaiņiem.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Zemi Tu esi dibinājis uz viņas pamatiem, ka tā nešaubās ne mūžam.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Ar jūras dziļumiem Tu to apsedzis kā ar apģērbu, ūdeņi stāvēja pār kalniem.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
No Taviem draudiem tie bēga, no Tava pērkona tie steidzās projām;
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Kalni cēlās un lejas nogrima tai vietā, ko Tu tām biji licis.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Tu esi licis robežas, tās tie (ūdeņi) nepārkāps un zemi vairs neapklās.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Tu izvadi avotus pa ielejām, ka tie tek starp kalniem.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Tie dzirdina visus lauka zvērus, tur atdzeras meža ēzeļi.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Pie tiem mīt debesputni, zaros tie dzied.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Tu slapini kalnus no augšienes; ar augļiem, ko Tu radi, zeme top piepildīta.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Tu liec zālei augt priekš lopiem un sējai cilvēkam par labu, lai nāk maize no zemes
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Un vīns, kas iepriecina cilvēka sirdi, ka viņa vaigs top skaistāks nekā no eļļas, un ka maize spēcina cilvēka sirdi.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Tā Kunga koki top papilnam slacināti, ciedra koki uz Lībanus, ko Viņš ir dēstījis.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Tur putni dara ligzdas un stārķi dzīvo uz priedēm.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Augstie kalni ir priekš mežu kazām, klintis kalna āpšiem par patvērumu.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Tu esi darījis mēnesi laikmetiem, saule zin savu noiešanu.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Tu dari tumsu, ka nakts metās; tad kustās visi meža zvēri.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Jaunie lauvas rūc pēc laupījuma, meklēdami savu barību no Dieva.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Un kad saule lec, tad tie atkal aizbēg un apguļas savās alās.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Tad cilvēks iziet pie sava darba, pie sava lauka darba līdz vakaram.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Cik lieli ir Tavi darbi, ak Kungs! Tos visus Tu esi darījis ar gudrību, - zeme ir Tava padoma pilna.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Redzi, jūra, liela un plata uz abējām pusēm! Tur mudžēt mudž neskaitāmā pulkā visādi zvēri, lieli, mazi.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Tur iet lielas laivas un Levijatans, ko Tu esi radījis, tur dzīvoties.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Tie visi uz Tevi gaida, ka Tu tiem barību dodi savā laikā.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Kad Tu tiem dod, tad tie salasa; kad Tu Savu roku atveri, tad tie ar labumu top pieēdināti.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Tu apslēpi Savu vaigu, tad tie iztrūkstas; Tu atņem viņiem dvašu, tad tie mirst un paliek atkal par pīšļiem.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Tu sūti Savu Garu, tad tie top radīti, un Tu atjauno zemes ģīmi.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Tā Kunga godība paliek mūžīgi; Tas Kungs priecājās par Saviem darbiem.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Viņš uzlūko zemi, tad tā dreb; Viņš aizskar kalnus, tad tie kūp.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Es dziedāšu Tam Kungam, kamēr es dzīvoju; es slavēšu savu Dievu ar dziesmām, kamēr šeit esmu.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Manas domas Viņam lai patīk; es priecāšos iekš Tā Kunga.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Grēcinieki no zemes lai izzūd un bezdievīgo lai vairs nav. Teici To Kungu, mana dvēsele, Alleluja.

< Zabura 104 >