< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
De David lui-même. Bénis, mon âme, le Seigneur: Seigneur mon Dieu, votre magnificence a paru avec un grand éclat. Vous avez revêtu la louange et l’honneur;
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Couvert de lumière comme d’un vêtement; Étendant le ciel comme une tente;
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Vous qui couvrez d’eaux sa partie la plus élevée, Qui montez sur un nuage, qui marchez sur les ailes des vents;
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Qui faites de vos anges des vents, et de vos ministres un feu brûlant;
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Qui avez fondé la terre sur sa base: elle ne sera pas ébranlée dans les siècles des siècles.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
L’abîme, comme un vêtement, l’enveloppe; des eaux s’élèveront au-dessus des montagnes.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
À votre réprimande elles s’enfuiront; à la voix de votre tonnerre, elles seront saisies d’une forte crainte.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Des montagnes s’élèvent, et des champs s’abaissent dans le lieu que vous leur avez fixé.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
C’est vous qui avez posé aux eaux un terme qu’elles ne dépasseront pas, et elles ne reviendront pas couvrir la terre.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Vous lâchez des fontaines dans les vallons: au milieu des montagnes traverseront les eaux.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Toutes les bêtes de la campagne s’abreuveront; les onagres soupireront après elles dans leur soif.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Au-dessus les oiseaux du ciel habiteront: du milieu des rochers ils feront entendre leurs voix.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Vous arrosez les montagnes avec les eaux supérieures du ciel: du fruit de vos ouvrages la terre sera rassasiée;
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Vous produisez du foin pour les bêtes, et de l’herbe à l’usage des hommes, Afin que vous fassiez sortir du pain de la terre,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Et que le vin réjouisse le cœur de l’homme: Afin qu’il égaie son visage avec l’huile, et que le pain fortifie le cœur de l’homme.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Ils seront abondamment nourris, les arbres de la campagne et les cèdres du Liban qu’il a plantés;
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Là des passereaux nicheront.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
De hautes montagnes servent de retraite aux cerfs; un rocher, de refuge aux hérissons.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Il a fait la lune pour marquer les temps; le soleil a connu son coucher.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Vous avez établi des ténèbres, et la nuit a été faite: c’est durant la nuit que feront leurs courses toutes les bêtes de la forêt.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Les petits des lions rugiront, cherchant une proie, et demandant à Dieu leur pâture.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Le soleil s’est levé, et ils se sont rassemblés; et ils se retireront dans leurs tanières.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Alors l’homme sortira pour son ouvrage, et pour son travail jusqu’au soir.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Combien magnifiques sont vos œuvres, Seigneur! Vous avez fait toutes choses avec sagesse: la terre est remplie de vos biens.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Cette mer est grande et spacieuse des deux côtés; là sont des reptiles sans nombre; Des animaux petits avec des grands;
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Là des navires traverseront.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Tous attendent de vous que vous leur donniez la nourriture au temps voulu.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Vous leur donnant, ils recueilleront: vous ouvrant votre main, tous seront remplis de vos biens.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Mais, vous détournant votre face, ils seront troublés: vous leur ôterez le souffle, et ils périront et retourneront dans leur poussière.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Vous enverrez votre esprit, et ils seront créés; et vous renouvellerez la face de la terre.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Soit la gloire du Seigneur à jamais célébrée: le Seigneur se réjouira dans ses œuvres,
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Lui qui regarde la terre et la fait trembler; qui touche les montagnes, et elles fument.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Je chanterai le Seigneur pendant ma vie: je jouerai du psaltérion en l’honneur de mon Dieu, tant que j’existerai.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Qu’agréable lui soit ma parole: pour moi, je mettrai mes délices dans le Seigneur.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Que les pécheurs disparaissent de la terre, ainsi que les hommes iniques, en sorte qu’ils ne soient plus: bénis, mon âme, le Seigneur.

< Zabura 104 >