< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Bénis, mon âme, l’Eternel! Eternel, mon Dieu, tu es infiniment grand; tu es vêtu de splendeur et de majesté.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Tu t’enveloppes de lumière comme d’un manteau, tu déploies les cieux comme une tenture.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Sur les eaux tu as posé les voûtes de ta demeure sublime, les nuages te servent de char, tu t’avances sur les ailes du vent.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Des vents tu fais tes messagers; des flammes ardentes, tes ministres.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Tu as fondé la terre sur ses colonnes d’appui, pour qu’elle ne chancelle jamais.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Tu l’as couverte de flots comme d’un vêtement; sur les montagnes les eaux s’étaient arrêtées.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
A ton injonction elles s’enfuirent; au bruit de ton tonnerre, elles s’élancèrent éperdues.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Des montagnes s’élevèrent, des vallées s’abaissèrent, occupant la place que tu leur avais assignée.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Tu leur as fixé des barrières infranchissables, pour les empêcher de submerger à nouveau la terre.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Tu fais jaillir des sources dans les vallées, elles poursuivent leur course entre les montagnes.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Elles abreuvent toutes les bêtes des champs, les onagres y étanchent leur soif.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Sur leurs bords, les oiseaux du ciel font leur demeure; d’entre la feuillée, ils élèvent leur ramage.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Du haut de ta résidence tu arroses les montagnes, la terre est nourrie du fruit de tes œuvres.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Tu fais croître l’herbe pour les animaux domestiques, des plantes pour l’usage de l’homme, en tirant sa nourriture du sein de la terre:
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
le vin qui réjouit le cœur des mortels, l’huile qui fait resplendir les visages, le pain enfin qui fortifie le cœur de l’homme.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Les arbres de l’Eternel sont abondamment pourvus, les cèdres du Liban que sa main a plantés.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Là les oiseaux bâtissent leurs nids, la cigogne fait des cyprès sa demeure.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Les montagnes escarpées servent de retraite aux chamois, les rochers de refuge aux gerboises.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Il a fait la lune pour marquer les temps, le soleil connaît le terme de sa course.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Tu amènes les ténèbres, et c’est la nuit, la nuit, où circulent tous les hôtes de la forêt.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Les lionceaux rugissent après la proie, demandant à Dieu leur pâture.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Le soleil commence à poindre, ils se retirent, et vont se blottir dans leurs tanières;
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
l’homme se rend à son labeur, accomplit sa besogne jusqu’au soir.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Que tes œuvres sont grandes, ô Seigneur! Toutes, tu les as faites avec sagesse; la terre est remplie de tes créations.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Voici le grand océan, aux étendues immenses! Là fourmillent des êtres sans nombre, des bêtes petites et grandes.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Là cheminent des navires, ce Léviathan que tu as formé pour s’y ébattre.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Tous mettent en toi leur attente, assurés que tu leur donneras leur nourriture en temps voulu.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Tu la leur donnes, ils la recueillent; tu ouvres la main, ils sont comblés de biens.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Tu dérobes ta face, ils sont dans l’épouvante; tu leur retires le souffle, ils expirent et retombent dans leur poussière.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Tu renvoies ton souffle, ils renaissent, et tu renouvelles la face de la terre!
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Que la gloire de l’Eternel dure à jamais! Que le Seigneur se réjouisse de ses œuvres!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Il regarde la terre, et elle vacille, il effleure les montagnes, et elles fument.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Je veux chanter l’Eternel ma vie durant, célébrer mon Dieu tant que j’existerai.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Puisse mon cantique lui être agréable! Moi, je me délecte en l’Eternel.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Que les pécheurs disparaissent de la terre, que les méchants ne soient plus! Mon âme, bénis l’Eternel, Alléluia!