< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
I give praise to Yahweh with all my life, Yahweh my God, you are very magnificent; you are clothed with splendor and majesty.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
You cover yourself with light as with a garment; you spread out the heavens like a tent curtain.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
You lay the beams of your chambers on the clouds; you make the clouds your chariot; you walk on the wings of the wind.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
He makes the winds his messengers, flames of fire his servants.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
He laid the foundations of the earth, and it will never be moved.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
You covered the earth with water like a garment; the water covered the mountains.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Your rebuke made the waters recede; at the sound of your thunderous voice they fled.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
The mountains rose, and the valleys spread out into the places that you had appointed for them.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
You have set a boundary for them that they will not cross; they will not cover the earth again.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
He made springs flow into the valleys; the streams flow between the mountains.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
They supply water for all the animals of the field; the wild donkeys quench their thirst.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
By the riverbanks the birds build their nests; they sing among the branches.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
He waters the mountains from his water chambers in the sky. The earth is filled with the fruit of his labor.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
He makes the grass grow for the cattle and plants for man to cultivate so that man may produce food from the earth.
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
He makes wine to make man happy, oil to make his face shine, and food to sustain his life.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
The trees of Yahweh get plenty of rain; the cedars of Lebanon which he planted.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
There the birds make their nests. The stork makes the cypress tree her home.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
The wild goats live on the high mountains; the mountain heights are a refuge for the hyraxes.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
He appointed the moon to mark the seasons; the sun knows its time for setting.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
You make the darkness of the night when all the beasts of the forest come out.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
The young lions roar for their prey and seek their food from God.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
When the sun rises, they retreat and sleep in their dens.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Meanwhile, people go out to their work and labor away until the evening.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Yahweh, how many and varied are your works! With wisdom you made them all; the earth overflows with your works.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Over there is the sea, deep and wide, teeming with innumerable creatures, both small and great.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
The ships travel there, and Leviathan is also there, which you formed to play in the sea.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
All these look to you to give them their food on time.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
When you give to them, they gather; when you open your hand, they are satisfied.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
When you hide your face, they are troubled; if you take away their breath, they die and return to dust.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
When you send out your Spirit, they are created, and you renew the countryside.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
May the glory of Yahweh last forever; may Yahweh enjoy his creation.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
He looks down on the earth, and it shakes; he touches the mountains, and they smoke.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
I will sing to Yahweh all my life; I will sing praise to my God as long as I live.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
May my thoughts be sweet to him; I will rejoice in Yahweh.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
May sinners vanish from the earth, and let the wicked be no more. I give praise to Yahweh with all my life. Praise Yahweh.