< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Bless the LORD, O my soul. O LORD my God, you are very great; you are clothed with honor and majesty.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Who cover yourself with light as with a garment: who stretch out the heavens like a curtain:
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Who lays the beams of his chambers in the waters: who makes the clouds his chariot: who walks on the wings of the wind:
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Who makes his angels spirits; his ministers a flaming fire:
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Who laid the foundations of the earth, that it should not be removed for ever.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
You covered it with the deep as with a garment: the waters stood above the mountains.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
At your rebuke they fled; at the voice of your thunder they hurried away.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
They go up by the mountains; they go down by the valleys to the place which you have founded for them.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
You have set a bound that they may not pass over; that they turn not again to cover the earth.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
He sends the springs into the valleys, which run among the hills.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
They give drink to every beast of the field: the wild asses quench their thirst.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
By them shall the fowls of the heaven have their habitation, which sing among the branches.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
He waters the hills from his chambers: the earth is satisfied with the fruit of your works.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
He causes the grass to grow for the cattle, and herb for the service of man: that he may bring forth food out of the earth;
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
And wine that makes glad the heart of man, and oil to make his face to shine, and bread which strengthens man’s heart.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
The trees of the LORD are full of sap; the cedars of Lebanon, which he has planted;
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Where the birds make their nests: as for the stork, the fir trees are her house.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
The high hills are a refuge for the wild goats; and the rocks for the conies.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
He appointed the moon for seasons: the sun knows his going down.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
You make darkness, and it is night: wherein all the beasts of the forest do creep forth.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
The young lions roar after their prey, and seek their meat from God.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
The sun rises, they gather themselves together, and lay them down in their dens.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Man goes forth to his work and to his labor until the evening.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
O LORD, how manifold are your works! in wisdom have you made them all: the earth is full of your riches.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
So is this great and wide sea, wherein are things creeping innumerable, both small and great beasts.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
There go the ships: there is that leviathan, whom you have made to play therein.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
These wait all on you; that you may give them their meat in due season.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
That you give them they gather: you open your hand, they are filled with good.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
You hide your face, they are troubled: you take away their breath, they die, and return to their dust.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
You send forth your spirit, they are created: and you renew the face of the earth.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
The glory of the LORD shall endure for ever: the LORD shall rejoice in his works.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
He looks on the earth, and it trembles: he touches the hills, and they smoke.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
I will sing to the LORD as long as I live: I will sing praise to my God while I have my being.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
My meditation of him shall be sweet: I will be glad in the LORD.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Let the sinners be consumed out of the earth, and let the wicked be no more. Bless you the LORD, O my soul. Praise you the LORD.

< Zabura 104 >