< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Bless the LORD, O my soul. O LORD my God, Thou art very great; Thou art clothed with glory and majesty.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Who coverest Thyself with light as with a garment, who stretchest out the heavens like a curtain;
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Who layest the beams of Thine upper chambers in the waters, who makest the clouds Thy chariot, who walkest upon the wings of the wind;
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Who makest winds Thy messengers, the flaming fire Thy ministers.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Who didst establish the earth upon its foundations, that it should not be moved for ever and ever;
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Thou didst cover it with the deep as with a vesture; the waters stood above the mountains.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
At Thy rebuke they fled, at the voice of Thy thunder they hasted away —
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
The mountains rose, the valleys sank down — unto the place which Thou hadst founded for them;
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Thou didst set a bound which they should not pass over, that they might not return to cover the earth.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Who sendest forth springs into the valleys; they run between the mountains;
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
They give drink to every beast of the field, the wild asses quench their thirst.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Beside them dwell the fowl of the heaven, from among the branches they sing.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Who waterest the mountains from Thine upper chambers; the earth is full of the fruit of Thy works.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Who causeth the grass to spring up for the cattle, and herb for the service of man; to bring forth bread out of the earth,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
And wine that maketh glad the heart of man, making the face brighter than oil, and bread that stayeth man's heart.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
The trees of the LORD have their fill, the cedars of Lebanon, which He hath planted;
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Wherein the birds make their nests; as for the stork, the fir-trees are her house.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
The high mountains are for the wild goats; the rocks are a refuge for the conies.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Who appointedst the moon for seasons; the sun knoweth his going down.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Thou makest darkness, and it is night, wherein all the beasts of the forest do creep forth.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
The young lions roar after their prey, and seek their food from God.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
The sun ariseth, they slink away, and couch in their dens.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Man goeth forth unto his work and to his labour until the evening.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
How manifold are Thy works, O LORD! In wisdom hast Thou made them all; the earth is full of Thy creatures.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Yonder sea, great and wide, therein are creeping things innumerable, living creatures, both small and great.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
There go the ships; there is leviathan, whom Thou hast formed to sport therein.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
All of them wait for Thee, that Thou mayest give them their food in due season.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Thou givest it unto them, they gather it; Thou openest Thy hand, they are satisfied with good.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Thou hidest Thy face, they vanish; Thou withdrawest their breath, they perish, and return to their dust.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Thou sendest forth Thy spirit, they are created; and Thou renewest the face of the earth.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
May the glory of the LORD endure for ever; let the LORD rejoice in His works!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Who looketh on the earth, and it trembleth; He toucheth the mountains, and they smoke.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
I will sing unto the LORD as long as I live; I will sing praise to my God while I have any being.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Let my musing be sweet unto Him; as for me, I will rejoice in the LORD.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Let sinners cease out of the earth, and let the wicked be no more. Bless the LORD, O my soul. Hallelujah.

< Zabura 104 >