< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
My soule, prayse thou the Lord: O Lord my God, thou art exceeding great, thou art clothed with glorie and honour.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Which couereth himselfe with light as with a garment, and spreadeth the heauens like a curtaine.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Which layeth the beames of his chambers in the waters, and maketh the cloudes his chariot, and walketh vpon the wings of the winde.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Which maketh his spirits his messengers, and a flaming fire his ministers.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
He set the earth vpon her foundations, so that it shall neuer moue.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Thou coueredst it with the deepe as with a garment: the waters woulde stand aboue the mountaines.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
But at thy rebuke they flee: at the voyce of thy thunder they haste away.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
And the mountaines ascend, and the valleis descend to the place which thou hast established for them.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
But thou hast set them a bounde, which they shall not passe: they shall not returne to couer the earth.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
He sendeth the springs into the valleis, which runne betweene the mountaines.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
They shall giue drinke to all the beasts of the fielde, and the wilde asses shall quench their thirst.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
By these springs shall the foules of the heauen dwell, and sing among the branches.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
He watereth the mountaines from his chambers, and the earth is filled with the fruite of thy workes.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
He causeth grasse to growe for the cattell, and herbe for the vse of man, that he may bring forth bread out of the earth,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
And wine that maketh glad the heart of man, and oyle to make the face to shine, and bread that strengtheneth mans heart.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
The high trees are satisfied, euen the cedars of Lebanon, which he hath planted,
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
That ye birdes may make their nestes there: the storke dwelleth in the firre trees.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
The high mountaines are for the goates: the rockes are a refuge for the conies.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
He appoynted the moone for certaine seasons: the sunne knoweth his going downe.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Thou makest darkenesse, and it is night, wherein all the beastes of the forest creepe forth.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
The lions roare after their praye, and seeke their meate at God.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
When the sunne riseth, they retire, and couche in their dennes.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Then goeth man forth to his worke, and to his labour vntill the euening.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
O Lord, howe manifolde are thy workes! in wisdome hast thou made them all: the earth is full of thy riches.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
So is this sea great and wide: for therein are things creeping innumerable, both small beastes and great.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
There goe the shippes, yea, that Liuiathan, whom thou hast made to play therein.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
All these waite vpon thee, that thou maiest giue them foode in due season.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Thou giuest it to them, and they gather it: thou openest thine hand, and they are filled with good things.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
But if thou hide thy face, they are troubled: if thou take away their breath, they dye and returne to their dust.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Againe if thou send forth thy spirit, they are created, and thou renuest the face of the earth.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Glory be to the Lord for euer: let the Lord reioyce in his workes.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
He looketh on the earth and it trembleth: he toucheth the mountaines, and they smoke.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
I will sing vnto the Lord all my life: I will prayse my God, while I liue.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Let my wordes be acceptable vnto him: I will reioyce in the Lord.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Let the sinners be consumed out of the earth, and the wicked till there be no more: O my soule, prayse thou the Lord. Prayse ye the Lord.

< Zabura 104 >