< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Bless the LORD, O my soul! O LORD my God, You are very great; You are clothed with splendor and majesty.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
He wraps Himself in light as with a garment; He stretches out the heavens like a tent,
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
laying the beams of His chambers in the waters above, making the clouds His chariot, walking on the wings of the wind.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
He makes the winds His messengers, flames of fire His servants.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
He set the earth on its foundations, never to be moved.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
You covered it with the deep like a garment; the waters stood above the mountains.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
At Your rebuke the waters fled; at the sound of Your thunder they hurried away—
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
the mountains rose and the valleys sank to the place You assigned for them—
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
You set a boundary they cannot cross, that they may never again cover the earth.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
He sends forth springs in the valleys; they flow between the mountains.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
They give drink to every beast of the field; the wild donkeys quench their thirst.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
The birds of the air nest beside the springs; they sing among the branches.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
He waters the mountains from His chambers; the earth is satisfied by the fruit of His works.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
He makes the grass grow for the livestock and provides crops for man to cultivate, bringing forth food from the earth:
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
wine that gladdens the heart of man, oil that makes his face to shine, and bread that sustains his heart.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
The trees of the LORD have their fill, the cedars of Lebanon that He planted,
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
where the birds build their nests; the stork makes her home in the cypresses.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
The high mountains are for the wild goats, the cliffs a refuge for the rock badgers.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
He made the moon to mark the seasons; the sun knows when to set.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
You bring darkness, and it becomes night, when all the beasts of the forest prowl.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
The young lions roar for their prey and seek their food from God.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
The sun rises, and they withdraw; they lie down in their dens.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Man goes forth to his work and to his labor until evening.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
How many are Your works, O LORD! In wisdom You have made them all; the earth is full of Your creatures.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Here is the sea, vast and wide, teeming with creatures beyond number, living things both great and small.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
There the ships pass, and Leviathan, which You formed to frolic there.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
All creatures look to You to give them their food in due season.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
When You give it to them, they gather it up; when You open Your hand, they are satisfied with good things.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
When You hide Your face, they are terrified; when You take away their breath, they die and return to dust.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
When You send Your Spirit, they are created, and You renew the face of the earth.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
May the glory of the LORD endure forever; may the LORD rejoice in His works.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
He looks on the earth, and it trembles; He touches the mountains, and they smolder.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
I will sing to the LORD all my life; I will sing praise to my God while I have my being.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
May my meditation be pleasing to Him, for I rejoice in the LORD.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
May sinners vanish from the earth and the wicked be no more. Bless the LORD, O my soul. Hallelujah!