< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Blagoslivljaj Jahvu, dušo moja, Jahve, Bože moj, silno si velik! Odjeven veličanstvom i ljepotom,
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
svjetlošću ogrnut kao plaštem! Nebo si razapeo kao šator,
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
na vodama sagradio dvorove svoje. Od oblaka praviš kola svoja, na krilima vjetrova putuješ.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Vjetrove uzimaš za glasnike, a žarki oganj za slugu svojega.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Zemlju si stavio na stupove njene: neće se poljuljati u vijeke vjekova,
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
pokrio si je vodama bezdanim k'o haljinom, iznad bregova stajahu vode;
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
na tvoju se prijetnju povukoše, od tvoje grmljavine zadrhtaše.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Bregovi se digoše, doline spustiše na mjesto koje si im odredio.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Odredio si granicu koju ne smiju prijeći, da opet ne pokriju zemlju.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Izvore svraćaš u potoke što žubore među brdima.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Oni poje sve živine poljske, divlji magarci žeđ gase u njima.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Uz njih se gnijezde ptice nebeske i pjevaju među granama.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Ti natapaš bregove iz dvorova svojih, zemlja se nasićuje plodom tvojih ruku.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Ti daješ te niče trava za stoku i bilje na korist čovjeku da izvede kruh iz zemlje
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
i vino što razvedruje srce čovječje; da uljem lice osvježi i da kruh okrijepi srce čovjeku.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Stabla se Jahvina napajaju hranom, cedri libanonski koje on zasadi.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Ondje se ptice gnijezde, u čempresu dom je rodin.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Visoki bregovi daju kozorogu a pećine jazavcu sklonište.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Ti si stvorio mjesec da označuje vremena i sunce znade kada ima zaći.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Kad razastreš tmine i noć se spusti, tad se šuljaju u njoj životinje šumske.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Lavići riču za plijenom i od Boga hranu traže.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Kad sunce ograne, nestaju i liježu na ležaje.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Tad čovjek izlazi na dnevni posao i na rad do večeri.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Kako su brojna tvoja djela, o Jahve! Sve si to mudro učinio: puna je zemlja stvorenja tvojih.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Eno mora, velika i široka, u njemu vrve gmazovi bez broja, životinje male i velike.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Onud prolaze nemani, Levijatan kojeg stvori da se igra u njemu.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
I sva ova bića željno čekaju da ih nahraniš na vrijeme.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Daješ li im, tada sabiru: otvaraš li ruku, nasite se dobrima.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Sakriješ li lice svoje, tad se rastuže; ako dah im oduzmeš, ugibaju i opet se u prah vraćaju.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Pošalješ li dah svoj, opet nastaju, i tako obnavljaš lice zemlje.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Neka dovijeka traje slava Jahvina: nek' se raduje Jahve u djelima svojim!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
On pogleda zemlju i ona se potrese, dotakne bregove, oni se zadime.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Pjevat ću Jahvi dokle god živim, svirat ću Bogu svome dokle god me bude.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Bilo mu milo pjevanje moje! Ja ću se radovati u Jahvi.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Nek' zločinci sa zemlje nestanu i bezbožnika nek' više ne bude! Blagoslivljaj Jahvu, dušo moja! Aleluja!