< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Aw ka hinglu, BOEIPA te uem lah. Ka BOEIPA Pathen namah tah na sang tangkik tih mueithennah neh rhuepomnah te na bai.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Khosae neh himbai bangla muelh aka thing uh himbaiyan bangla vaan ah dup aka phaih,
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
A imhman te tui soah aka ci, khomai te leng la aka saii, khohli phae neh aka cet,
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
khohli te a puencawn la aka saii tih hmai tak aka tueih loh,
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
diklai khaw amah hmuen ah a suen tih kumhal ah tuen yoeyah pawh.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Anih te tuidung neh pueinak bangla na khuk tih tui rhoek loh tlang rhoek soah pai uh.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Namah kah tluungnah dongah rhaelrham uh tih na khohum ol dongah tamto uh.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Tlang tom a lan uh tih amih ham na suen kolbawn hmuen la suntla uh.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Khorhi na suem te a poe uh thai pawt dongah diklai khuk ham ha mael uh thai pawh.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Tuisih rhoek te soklong la a loei tlang rhoek laklo ah long uh.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Kohong kah mulhing boeih te tui a tul uh tih kohong marhang rhoek khaw a tuihalh dip uh.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
A taengah vaan kah vaa loh kho a sak uh tih thingsam laklo ah a ol huphup loei.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Tlang boeih te a imhman lamkah aka suep, BOEIPAnamah kah kutci loh diklai te a hah sak.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Rhamsa ham sulrham poe tih, hlang kah thohtatnah hamla baelhing neh, diklai lamkah buh na thoeng sak.
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Te dongah misurtui loh hlanghing thinko ko a hoe sak, situi loh maelhmai a hlampan sak tih buh loh hlanghing thinko a duel.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
BOEIPA loh a ling thingkung, Lebanon kah lamphai te a kum sakuh.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Teah te vaa loh bu a tuk tih, bungrho loh hmaical dongah a im a khueh.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Tlang sang boeih te sathai ham om tih, pango boeih khaw saphih ham hlipyingnah la om.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Khoning ham hla a saii tih khomik loh a khotlak khaw a ming.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Khohmuep na khueh tih khoyin ha pawk vaengah duup kah mulhing boeih loh a khuiah yuel uh.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Maeh te sathueng rhoek loh a kawk thil uh tih a caak te Pathen taengah a tlap uh.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Khomik a thoeng neh vawl khoem uh tih a khuisaek la kol uh.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Hlang he a bisai ham neh a thohtatnah la kholaeh hil cet.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
BOEIPA nang kah kutngo he yet tangkik. Te rhoek boeih te cueihnah nen ni na saii. Na hnopai rhoemah diklai ah baetawt coeng.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Tuitunli aka len tih a dang, aka dangka ah, rhulcai mulhing a yit a len tae lek pawt la om bal.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Teah te sangpho rhoek loh pongpa uh tih a khuiah aka luem ham Leviathan te na saii.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
A tuetang vaengah amih caak paek ham khaw amih loh namah taengla boeih lamso uh.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Amih taengah na paek te a rhuh uh. Na kut na hlam tih hnothen kum uh.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Na maelhmai na thuh vaengah let uh. A hil na khoem pah vaengah pal uh tih laipi la bal uh.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Na mueihla na tueih daengah anmih te suen uh tih diklai maelhmai khaw na tlaih pueng.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
BOEIPA kah thangpomnah tah kumhal duela om tih, a bibi dongah BOEIPA a kohoe saeh.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Diklai a paelki vaengah thuen tih, tlang rhoek te a taek vaengah khuu.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Ka hingnah neh BOEIPA te ka hlai vetih ka om rhuet vaengah ka Pathen te ka tingtoeng ni.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Ka olding he anih ham a lungtui saeh. Kai tah BOEIPA dongah ka kohoe coeng.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Hlangtholh rhoek te diklai lamloh mitmoeng uh saeh lamtah halang rhoek khaw koep om boel saeh. Aw ka hinglu, BOEIPA tah a yoethen pai saeh tila BOEIPA te thangthen lah.

< Zabura 104 >