< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
En Psalm Davids. Lofva Herran, min själ, och allt det uti mig är, hans helga Namn.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Lofva Herran, min själ, och förgät icke, hvad godt han dig gjort hafver;
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Den dig alla dina synder förlåter, och helar alla dina brister;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Den ditt lif förlöser ifrå förderf, och kröner dig med nåd och barmhertighet;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Den dig uppfyller med tröst, att du dägelig varder, och gör dig ung och frisk såsom en örn.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Herren skaffar rättfärdighet och dom, allom dem som orätt lida.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Han hafver låtit Mose veta sina vägar; Israels barn sin verk.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Barmhertig och nådelig är Herren, tålig och af stora mildhet.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Han träter icke till evig tid, och vredgas icke evinnerliga.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Han handlar icke med oss efter våra synder, och vedergäller oss icke efter våra missgerningar.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Ty så hög som himmelen öfver jordena är, låter han sina nåd väldig vara öfver dem som frukta honom.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Så långt som öster är ifrå vester, låter han vår öfverträdelse vara ifrån oss.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Såsom en fader förbarmar sig öfver barnen, så förbarmar sig Herren öfver dem som frukta honom.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Ty han vet hvad vi för ett verk äre; han tänker derpå, att vi stoft äre.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
En menniska är i sitt lefvande såsom gräs; hon blomstras såsom ett blomster på markene.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
När vädret deröfver går, så är det intet mer der, och dess rum känner det intet mer.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Men Herrans nåd varar ifrån evighet till evighet, öfver dem som frukta honom; och hans rättfärdighet intill barnabarn,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
När dem som hans förbund hålla, och tänka uppå hans bud, att de derefter göra.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Herren hafver beredt sin stol i himmelen, och hans rike skall råda öfver allt.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Lofver Herran, I hans Änglar, I starke hjeltar, som hans befallning uträtten, att man hans ords röst höra skall.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Lofver Herran, alle hans härar; I hans tjenare, som hans vilja gören.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Lofver Herran, all hans verk uti all hans herradömes rum; min själ lofve Herran.