< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Bendice, alma mía, a Yavé, Y bendiga todo mi ser su santo Nombre.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bendice, alma mía, a Yavé, Y no olvides ninguno de sus beneficios.
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Él es Quien perdona todas tus iniquidades, Quien sana todas tus dolencias,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Quien rescata del hoyo tu vida, Quien te corona de misericordia y compasión,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Quien sacia tu boca con buenas cosas, De modo que te rejuvenezcas como el águila.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Yavé es Quien hace justicia Y juicios justos para todos los oprimidos.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Dio a conocer sus caminos a Moisés, Y a los hijos de Israel sus obras.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Compasivo y bondadoso es Yavé, Lento para la ira y grande en misericordia.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
No contenderá para siempre, Ni para siempre guardará [el enojo].
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
No nos trató según nuestras iniquidades, Ni nos retribuyó según nuestros pecados.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Porque como la altura de los cielos sobre la tierra, Engrandeció su misericordia hacia los que le temen.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Tan lejos como está el oriente del occidente Removió de nosotros nuestras transgresiones.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Como un padre tiene compasión de [sus] hijos, Así Yavé tiene compasión de los que le temen.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Porque Él conoce nuestra condición. Se acuerda de que somos polvo.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Como la hierba son los días del hombre. Florece como una flor del campo.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Cuando el viento pasa sobre ella, ya no existe, Y su lugar ya no la reconoce.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Pero la misericordia de Yavé es desde la eternidad Hasta la eternidad sobre los que le temen, Y su justicia sobre los hijos de los hijos,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Sobre los que observan su Pacto Y recuerdan sus Preceptos para practicarlos.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Yavé estableció en los cielos su trono, Y su reino domina sobre todo.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bendigan a Yavé, ustedes sus ángeles, Poderosos en fortaleza, Que ejecutan su Palabra, Al obedecer la voz de su mandato.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bendigan a Yavé, ustedes todas sus huestes, Ministros suyos que hacen su voluntad.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bendigan a Yavé ustedes, todas sus obras, En todos los lugares de su señorío. Bendice, oh alma mía, a Yavé.