< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
ipsi David benedic anima mea Domino et omnia quae intra me sunt nomini sancto eius
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
benedic anima mea Domino et noli oblivisci omnes retributiones eius
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
qui propitiatur omnibus iniquitatibus tuis qui sanat omnes infirmitates tuas
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
qui redimit de interitu vitam tuam qui coronat te in misericordia et miserationibus
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
qui replet in bonis desiderium tuum renovabitur ut aquilae iuventus tua
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
faciens misericordias Dominus et iudicium omnibus iniuriam patientibus
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
notas fecit vias suas Mosi filiis Israhel voluntates suas
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
miserator et misericors Dominus longanimis et multum misericors
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
non in perpetuum irascetur neque in aeternum comminabitur
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
non secundum peccata nostra fecit nobis nec secundum iniustitias nostras retribuit nobis
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
quoniam secundum altitudinem caeli a terra corroboravit misericordiam suam super timentes se
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
quantum distat ortus ab occidente longe fecit a nobis iniquitates nostras
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
quomodo miseretur pater filiorum misertus est Dominus timentibus se
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
quoniam ipse cognovit figmentum nostrum recordatus est quoniam pulvis sumus
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
homo sicut faenum dies eius tamquam flos agri sic efflorebit
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
quoniam spiritus pertransivit in illo et non subsistet et non cognoscet amplius locum suum
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
misericordia autem Domini ab aeterno et usque in aeternum super timentes eum et iustitia illius in filios filiorum
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
his qui servant testamentum eius et memores sunt mandatorum ipsius ad faciendum ea
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Dominus in caelo paravit sedem suam et regnum ipsius omnibus dominabitur
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
benedicite Domino angeli eius potentes virtute facientes verbum illius ad audiendam vocem sermonum eius
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
benedicite Domino omnes virtutes eius ministri eius qui facitis voluntatem eius
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
benedicite Domino omnia opera eius in omni loco dominationis ipsius benedic anima mea Domino