< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Dari Daud. Pujilah TUHAN, hai jiwaku, segenap batinku, pujilah nama-Nya yang kudus.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Pujilah TUHAN, hai jiwaku, jangan lupakan segala kebaikan-Nya!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Dia yang mengampuni semua dosamu, yang menyembuhkan segala penyakitmu,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Dia yang membebaskan nyawamu dari kuburan, yang melimpahi engkau dengan kasih dan belas kasihan.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Dia yang memuaskan hidupmu dengan yang baik, sehingga engkau awet muda seperti burung rajawali.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
TUHAN menjalankan hukum dan keadilan bagi semua orang yang tertindas.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Ia menyatakan rencana-Nya kepada Musa dan perbuatan-perbuatan-Nya kepada bangsa Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Sebab TUHAN pengasih dan penyayang, Ia panjang sabar dan kasih-Nya berlimpah.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Ia tidak menghardik terus-menerus, dan tidak marah untuk selama-lamanya.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Ia tidak menghukum kita setimpal dosa kita, atau membalas kita setimpal kesalahan kita.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Tetapi setinggi langit di atas bumi, sebesar itu kasih-Nya bagi orang yang takwa.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Sejauh timur dari barat, sejauh itu dibuang-Nya dosa-dosa kita.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Seperti seorang bapak mengasihi anak-anaknya, begitulah TUHAN mengasihi orang yang takwa.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Sebab TUHAN tahu kita terbuat dari apa, Ia ingat kita ini hanya debu.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Manusia hidupnya singkat seperti rumput; ia berkembang seperti bunga di ladang;
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
bila ditiup angin, lenyaplah ia, malah tempatnya tidak diketahui lagi.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Tetapi TUHAN tetap mengasihi orang takwa, kebaikan-Nya berlangsung turun-temurun
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
bagi orang yang berpegang pada perjanjian-Nya, dan dengan setia melakukan perintah-Nya.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
TUHAN memerintah di surga, Ia raja yang berkuasa atas segala-galanya.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Pujilah TUHAN, hai malaikat-malaikat-Nya yang perkasa, yang mendengarkan dan melakukan perintah-Nya.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Pujilah TUHAN, hai semua makhluk di surga, semua hamba-Nya yang melakukan kehendak-Nya.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Pujilah TUHAN, hai segala ciptaan di seluruh wilayah kekuasaan-Nya. Pujilah TUHAN, hai jiwaku!

< Zabura 103 >