< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Von David. Preise, meine Seele, Jahwe, und alles, was in mir ist, seinen heiligen Namen!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Preise, meine Seele, Jahwe, und vergiß nicht, was er dir alles gethan hat!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Der dir alle deine Schuld vergab, alle deine Gebrechen heilte,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
der dein Leben aus der Grube erlöste, mit Gnade und Barmherzigkeit dich krönte,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
der dein Verlangen mit Gutem sättigte; dem Adler gleich erneuert sich deine Jugend!
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Gerechtigkeit schafft Jahwe und Recht für alle Unterdrückten.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Er ließ seine Wege Mose kund werden, den Söhnen Israels seine großen Thaten.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Barmherzig und gnädig ist Jahwe, langsam zum Zorn und reich an Huld.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Nicht für immer hadert er, noch trägt er ewig nach.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Er verfuhr mit uns nicht nach unseren Sünden und vergalt uns nicht nach unseren Verschuldungen,
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
sondern so hoch der Himmel über der Erde ist, ist seine Gnade mächtig über denen, die ihn fürchten.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
So fern der Sonnenaufgang vom Untergang, hat er unsere Vergehungen von uns entfernt.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Wie sich ein Vater über Kinder erbarmt, hat sich Jahwe erbarmt über die, die ihn fürchten.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Denn er weiß, woraus wir geformt sind, ist eingedenk, daß wir Staub sind.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Des Menschen Lebenstage sind wie das Gras; wie eine Blume auf dem Felde, also blüht er.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Wenn ein Windhauch über ihn dahingefahren, ist er dahin, und seine Stätte kennt ihn nicht mehr.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Die Gnade Jahwes aber währt von Ewigkeit zu Ewigkeit über denen, die ihn fürchten, und seine Gerechtigkeit auf Kindeskinder
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
derer, die seinen Bund halten und seiner Gebote eingedenk sind, daß sie danach thun.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Jahwe hat seinen Thron im Himmel aufgerichtet, und sein Königtum herrscht über das All.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Preist Jahwe, ihr, seine Engel, ihr starken Helden, die ihr seinen Befehl ausrichtet, indem sie auf den Schall seines Wortes hören.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Preist Jahwe, ihr, all sein Heer, seine Diener, die ihr seinen Willen vollzieht.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Preist Jahwe, alle seine Werke an allen Orten seiner Herrschaft. Preise, meine Seele, Jahwe!

< Zabura 103 >