< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Von David. Preise Jehova, meine Seele, und all mein Inneres seinen heiligen Namen!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Preise Jehova, meine Seele, und vergiß nicht alle seine Wohltaten!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Der da vergibt alle deine Ungerechtigkeit, der da heilt alle deine Krankheiten;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
der dein Leben erlöst von der Grube, der dich krönt mit Güte und Erbarmungen;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
der mit Gutem sättigt dein Alter; deine Jugend erneuert sich wie die des Adlers.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Jehova übt Gerechtigkeit und schafft Recht allen, die bedrückt werden.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Er tat seine Wege kund dem Mose, den Kindern Israel seine Taten.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Barmherzig und gnädig ist Jehova, langsam zum Zorn und groß an Güte;
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Er wird nicht immerdar rechten und nicht ewiglich nachtragen.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Er hat uns nicht getan nach unseren Sünden, und nach unseren Ungerechtigkeiten uns nicht vergolten.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Denn so hoch die Himmel über der Erde sind, ist gewaltig seine Güte über die, welche ihn fürchten;
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
so weit der Osten ist vom Westen, hat er von uns entfernt unsere Übertretungen.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Wie ein Vater sich über die Kinder erbarmt, so erbarmt sich Jehova über die, welche ihn fürchten.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Denn er kennt unser Gebilde, ist eingedenk, daß wir Staub sind.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Der Mensch, wie Gras sind seine Tage; wie die Blume des Feldes, also blüht er.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Denn ein Wind fährt darüber, und sie ist nicht mehr, und ihre Stätte kennt sie nicht mehr.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Die Güte Jehovas aber ist von Ewigkeit zu Ewigkeit über die, welche ihn fürchten, und seine Gerechtigkeit auf Kindeskinder hin;
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
für die, welche seinen Bund halten, und seiner Vorschriften gedenken, um sie zu tun.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Jehova hat in den Himmeln festgestellt seinen Thron, und sein Reich herrscht über alles.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Preiset Jehova, ihr seine Engel, ihr Gewaltigen an Kraft, Täter seines Wortes, gehorsam der Stimme seines Wortes!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Preiset Jehova, alle seine Heerscharen, ihr seine Diener, Täter seines Wohlgefallens!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Preiset Jehova, alle seine Werke, an allen Orten seiner Herrschaft! Preise Jehova, meine Seele!