< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Von David. / Preise Jahwe, o meine Seele, / Und all mein Innres seinen heiligen Namen!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Preise Jahwe, o meine Seele, / Und vergiß nicht all seiner Segenstaten!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Er vergibt dir all deine Missetat, / Schafft all deiner Krankheit Heilung.
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Er erlöset dein Leben vom Tode, / Krönt dich mit Huld und Erbarmen.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Er sättigt dein Alter mit Gutem, / So daß deine Jugend sich wieder erneut / Wie eines Adlers Gefieder.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Heilstaten vollführet Jahwe, / Recht schafft er allen Bedrückten.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Mose tat er seine Wege kund, / Israels Söhnen sein herrliches Tun.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Barmherzig und gnädig ist Jahwe, / Langmütig und reich an Huld.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Er hat nicht für immer gehadert / Und nicht auf ewig gezürnt.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Nicht nach unsern Sünden hat er uns gelohnt, / Uns nicht vergolten nach unsern Vergehn.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Sondern so hoch der Himmel ist über der Erde, / So mächtig war seine Huld bei den Frommen.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
So weit der Osten vom Westen ist, / Hat er unsre Frevel von uns entfernt.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Wie sich ein Vater der Kinder erbarmt, / Hat Jahwe sich stets erbarmt seiner Frommen.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Er weiß ja, wie schwach wir sind, / Er gedenket daran: wir sind Staub.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Eines Sterblichen Tage sind wie Gras, / Wie des Feldes Blume, so blüht er.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Fährt über sie ein Windstoß, so ist sie dahin, / Und es kennt sie nicht mehr ihre Stätte.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Doch Jahwes Gnade erzeigt sich auf ewig an seinen Frommen, / Seine Treue erfahren in jedem Geschlecht
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Alle, die seinen Bund bewahren / Und seiner Gebote gedenken, sie zu erfüllen.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Jahwe hat seinen Thron im Himmel errichtet, / Sein Königtum herrscht über alles.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Preist Jahwe, ihr seine Engel, / Ihr Helden an Kraft, die ihr sein Gebot vollführt, / Indem ihr dem Ruf seines Wortes gehorcht!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Preist Jahwe, ihr seine Heere alle, / Seine Diener, die ihr seinen Willen vollstreckt!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Preist Jahwe, ihr seine Werke all, / An jedem Ort seines Herrschaftsgebiets! / Preise Jahwe auch meine Seele!

< Zabura 103 >