< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
De David lui-même.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bénis, mon âme, le Seigneur, et n’oublie point ses bienfaits.
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
C’est lui qui pardonne toutes tes iniquités; lui qui guérit toutes tes infirmités.
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
C’est lui qui rachète de la mort ta vie; qui te couronne de miséricorde et de bontés.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
C’est lui qui remplit de biens ton désir: ta jeunesse sera renouvelée comme celle de l’aigle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Le Seigneur fait miséricorde et justice à tous ceux qui souffrent une injustice.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Il a fait connaître ses voies à Moïse, aux enfants d’Israël ses volontés.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Compatissant et miséricordieux est le Seigneur; lent à punir et bien miséricordieux.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Il ne sera pas perpétuellement irrité; et éternellement il ne menacera pas.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Ce n’est pas selon nos péchés qu’il nous a traités; ni selon nos iniquités qu’il nous a rétribués.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Puisque, selon la hauteur des cieux au-dessus de la terre, il a corroboré sa miséricorde sur ceux qui le craignent.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Autant est distant l’orient de l’occident, autant il a éloigné de nous nos iniquités.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
De même qu’un père s’attendrit sur ses enfants, de même le Seigneur a eu pitié de ceux qui le craignent;
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Parce que lui-même sait de quoi nous sommes formés. Il s’est souvenu que nous sommes poussière;
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Un homme, ses jours sont comme une herbe: comme une fleur des champs, ainsi il fleurira.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Parce qu’un souffle passera sur elle, et elle ne subsistera pas: et on ne connaîtra plus son lieu.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Mais la miséricorde du Seigneur est de l’éternité et jusqu’à l’éternité sur ceux qui le craignent.
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Pour ceux qui gardent son alliance. Et se souviennent de ses commandements, pour les accomplir.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Le Seigneur dans le ciel a préparé son trône; et son empire dominera sur toutes choses.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bénissez le Seigneur, vous tous ses anges, puissants en force, accomplissant sa parole, pour obéir à la voix de ses ordres.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bénissez le Seigneur, vous toutes ses armées célestes; vous ses ministres, qui faites sa volonté.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bénissez le Seigneur, vous tous ses ouvrages, dans tous les lieux de sa domination: bénis, mon âme, le Seigneur.