< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Psaume de David. Mon âme, bénis l'Éternel, Et que tout ce qui est en moi bénisse son saint nom!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Mon âme, bénis l'Éternel, Et n'oublie aucun de ses bienfaits!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
C'est lui qui pardonne toutes tes iniquités. Qui guérit toutes tes infirmités,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Qui arrache ta vie au tombeau. Qui te couronne de bonté et de miséricorde.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
C'est lui qui comble de biens ta vieillesse. Et qui renouvelle ta jeunesse comme celle de l'aigle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
L'Éternel fait justice Et droit à tous les opprimés.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Il a révélé ses desseins à Moïse, Et il a montré sa puissance aux enfants d'Israël.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
L'Éternel est compatissant et miséricordieux. Lent à la colère et riche en bonté.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Il n'accuse pas toujours; Il ne garde pas son courroux à perpétuité.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Il ne nous a pas traités selon nos péchés. Et il ne nous a pas punis selon nos iniquités.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
En effet, autant les cieux sont élevés au-dessus de la terre. Autant sa bonté est grande pour ceux qui le craignent.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Il a éloigné de nous nos transgressions. Autant que l'Orient est éloigné de l'Occident.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Comme un père est ému de compassion envers ses enfants, L'Éternel est ému de compassion envers ceux qui le craignent.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Car il sait bien de quoi nous sommes faits: Il se souvient que nous ne sommes que poussière!
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Les jours de l'homme sont comme l'herbe; Il fleurit comme la fleur des champs:
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Que le vent souffle sur elle, et voici qu'elle n'est plus; La place où elle était ne la connaît plus!
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Mais la bonté de l'Éternel, pour ceux qui le craignent, Subsiste de tout temps et à toujours; Et il accorde sa délivrance aux enfants de leurs enfants,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
A tous ceux qui gardent son alliance Et se rappellent ses commandements, Afin de les mettre en pratique.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
L'Éternel a établi son trône dans les cieux, Et tout est soumis à son empire.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bénissez l'Éternel, vous, ses anges forts et vaillants, Qui exécutez son commandement, Et qui obéissez à sa voix!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bénissez l'Éternel, vous, toutes ses armées. Qui êtes à son service et qui faites sa volonté!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bénissez l'Éternel, vous, toutes ses oeuvres. Dans tous les lieux de son empire! Mon âme, bénis l'Éternel!