< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Psaume de David. Mon âme, bénis l'Éternel, et que tout ce qui est en moi bénisse son saint nom!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Mon âme, bénis l'Éternel, et n'oublie aucun de ses bienfaits!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
C'est lui qui pardonne toutes tes iniquités; qui guérit toutes tes infirmités;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Qui retire ta vie de la fosse; qui te couronne de bonté et de compassion;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Qui rassasie ta bouche de biens, tellement que ta jeunesse est renouvelée comme celle de l'aigle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
L'Éternel fait justice et droit à tous ceux qui sont opprimés.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Il a fait connaître ses voies à Moïse, et ses exploits aux enfants d'Israël.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
L'Éternel est compatissant et miséricordieux; lent à la colère et abondant en grâce.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Il ne conteste pas à perpétuité, et ne garde pas sa colère à toujours.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Il ne nous a pas fait selon nos péchés, et ne nous a pas rendu selon nos iniquités.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Car autant les cieux sont élevés au-dessus de la terre, autant sa bonté est grande sur ceux qui le craignent.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Il a éloigné de nous nos iniquités, autant que l'orient est éloigné de l'occident.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Comme un père est ému de compassion envers ses enfants, l'Éternel est ému de compassion envers ceux qui le craignent.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Car il connaît de quoi nous sommes faits, il se souvient que nous ne sommes que poussière.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Les jours de l'homme sont comme l'herbe; il fleurit comme la fleur des champs.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Car le vent ayant passé dessus, elle n'est plus, et son lieu ne la reconnaît plus.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Mais la bonté de l'Éternel est de tout temps et à toujours sur ceux qui le craignent, et sa justice pour les enfants de leurs enfants,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Pour ceux qui gardent son alliance et se souviennent de ses commandements pour les accomplir.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
L'Éternel a établi son trône dans les cieux, et son règne a la domination sur tout.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bénissez l'Éternel, vous ses anges puissants en force, qui exécutez son commandement en obéissant à la voix de sa parole!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bénissez l'Éternel, vous toutes ses armées, qui êtes ses serviteurs, et qui faites sa volonté!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bénissez l'Éternel, vous toutes ses œuvres, dans tous les lieux de son empire! Mon âme, bénis l'Éternel!

< Zabura 103 >