< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
[I tell] myself that I should praise Yahweh. I will praise him [MTY] with all of my inner being, [because] he [MTY] is holy.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
[I tell] myself that I should praise Yahweh and never forget all the kind things he has done for me:
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
He forgives all my sins, and he heals me from all my diseases/sicknesses;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
he keeps me from dying [MTY], and blesses me by faithfully loving me and acting mercifully to me.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
He gives me good things during my entire life. He makes me feel young and strong like eagles.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Yahweh judges justly and (vindicates/does what is right for) all those who have been treated unfairly.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
[Long ago] he revealed to Moses what he planned to do; he showed to the [ancestors of us] Israeli people the mighty things that he was able to do.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Yahweh acts mercifully and kindly; he does not quickly (get angry/punish us) [when we sin]; he is always [showing us that he] faithfully loves us.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He will not keep rebuking us, and he will not remain angry forever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He punishes us for our sins, but he does not punish us [severely] as we deserve [DOU]!
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
The skies are very high above the earth, and Yahweh’s faithful love for all those who revere him is just as great.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
He has taken away [the guilt for] [MTY] our sins, taking it as far from us as the east is from the west.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Just like parents act mercifully toward their children, Yahweh is kind to those who revere him.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
He knows what our bodies are like; he remembers that [he created us from] dirt, and so we quickly fail [to do what pleases him] [MET].
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
We humans do not live forever [SIM]; we are like grass [SIM] [that withers and dies]. We are like wild flowers: They bloom [for a short while],
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
but then the [hot] wind blows over them, and they disappear; no one sees them again.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But Yahweh will faithfully keep loving forever all those who revere him. He will act fairly to our children and to their children;
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
he will act that way to all those who obey the agreement he made with them [to bless them if they did what he told them to do], to all those who obey what he has commanded.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Yahweh made/caused the heavens to be the place where he rules [MTY]; from there he rules over everything.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
You angels who belong to Yahweh, praise him! You are powerful creatures/beings who do what he tells you to do; you obey what he commands.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Praise Yahweh, you armies/thousands of angels who serve him and do what he desires!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
All you things that Yahweh has created, praise him; praise him in every place where he rules, everywhere! And I [also] will praise Yahweh!

< Zabura 103 >