< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Bless, O my soul, Yahweh, —And all that is within me, his holy Name;
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bless, O my soul, Yahweh, And forget not all his dealings: —
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Who forgiveth all thine iniquity, Who healeth all thy diseases;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Who redeemeth, from destruction, thy life, Who crowneth thee, with lovingkindness and compassion:
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Who satisfieth, with good, thine age, Thy youth, reneweth itself like an eagle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Yahweh is one, who executeth righteousness, Yea vindication for all the oppressed.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Who made known his ways unto Moses, unto the sons of Israel, his doings.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Compassionate and gracious, is Yahweh, —Slow to anger and abundant in lovingkindness.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Not perpetually, will he contend, Nor age-abidingly, retain anger;
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Not according to our sins, hath he dealt with us, Nor according to our iniquities, hath he treated us.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
For, as the heavens are exalted over the earth, His lovingkindness hath prevailed over them who revere him;
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as East from West, Hath he put far from us, our transgressions;
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Like the compassion of a father for his children, Is, the compassion of Yahweh, for them who revere him;
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For, he, knoweth how we are formed, He is mindful that, dust, we are.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
As for man, like grass, are his days, Like the blossom of the field, so, doth he blossom;
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
For, a wind, hath passed over it, and it is gone, And its own place is acquainted with it no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But, the lovingkindness of Yahweh, is from one age even to another, Upon them who revere him, And his righteousness, to children’s children: —
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
To such as keep his covenant, And remember his precepts, to do them.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Yahweh, in the heavens, hath established his throne, And, his kingdom, over all, hath dominion.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bless Yahweh, ye messengers of his, —Heroes of vigour, doing his word, To hearken [again] to the voice of his word;
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bless Yahweh, all ye his hosts, Attendants of his, doing his pleasure;
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bless Yahweh, all ye his works, In all places of his dominion, Bless, O my soul, Yahweh.