< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
“A psalm of David.” Bless the LORD, O my soul! And all that is within me, bless his holy name!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bless the LORD, O my soul! And forget not all his benefits!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Who forgiveth all thine iniquities; Who healeth all thy diseases;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Who redeemeth thy life from the grave; Who crowneth thee with loving-kindness and tender mercies;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Who satisfieth thine old age with good, So that thy youth is renewed like the eagle's.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
The LORD executeth justice And equity for all the oppressed.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
He made known his ways to Moses, His doings to the children of Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
The LORD is merciful and kind, Slow to anger and rich in mercy.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He doth not always chide, Nor doth he keep his anger for ever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He hath not dealt with us according to our sins, Nor requited us according to our iniquities.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
As high as are the heavens above the earth, So great is his mercy to them that fear him.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as the east is from the west, So far hath he removed our transgressions from us.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Even as a father pitieth his children, So the LORD pitieth them that fear him.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For he knoweth our frame, He remembereth that we are dust.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
As for man, his days are as grass; As a flower of the field, so he flourisheth.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
The wind passeth over it, and it is gone; And its place shall know it no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But the mercy of the LORD is from everlasting to everlasting to them that fear him, And his righteousness to children's children,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
To such as keep his covenant, And remember his commandments to do them.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
The LORD hath established his throne in the heavens, And his kingdom ruleth over all.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bless the LORD, ye his angels, Ye mighty ones who do his commands, Hearkening to the voice of his word!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bless the LORD, all ye his hosts; Ye, his ministers, who do his pleasure!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bless the LORD, all his works, In all places of his dominion! Bless the LORD, O my soul!

< Zabura 103 >