< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
For David himself. Bless the Lord, O my soul: and let all that is within me bless his holy name.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bless the Lord, O my soul, and never forget all he hath done for thee.
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Who forgiveth all thy iniquities: who healeth all thy diseases.
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
Who redeemeth thy life from destruction: who crowneth thee with mercy and compassion.
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
Who satisfieth thy desire with good things: thy youth shall be renewed like the eagle’s.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
The Lord doth mercies, and judgment for all that suffer wrong.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
He hath made his ways known to Moses: his wills to the children of Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
The ford is compassionate and merciful: longsuffering and plenteous in mercy.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He will not always be angry: nor will he threaten for ever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He hath not dealt with us according to our sins: nor rewarded us according to our iniquities.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
For according to the height of the heaven above the earth: he hath strengthened his mercy towards them that fear him.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as the east is from the west, so far hath he removed our iniquities from us.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
As a father hath compassion on his children, so hath the Lord compassion on them that fear him:
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For he knoweth our frame. He remembereth that we are dust:
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Man’s days are as grass, as the flower of the field so shall he flourish.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
For the spirit shall pass in him, and he shall not be: and he shall know his place no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But the mercy of the Lord is from eternity and unto eternity upon them that fear him: And his justice unto children’s children,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
To such as keep his covenant, And are mindful of his commandments to do them.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
The Lord hath prepared his throne in heaven: and his kingdom shall rule over all.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bless the Lord, all ye his angels: you that are mighty in strength, and execute his word, hearkening to the voice of his orders.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bless the Lord, all ye his hosts: you ministers of his that do his will.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bless the Lord, all his works: in every place of his dominion, O my soul, bless thou the Lord.

< Zabura 103 >