< Zabura 103 >
1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Bless Jehovah, O my soul, and all that is within me, bless his holy name.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bless Jehovah, O my soul, and forget not all his benefits,
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
who forgives all thine iniquities, who heals all thy diseases,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
who redeems thy life from destruction, who crowns thee with loving kindness and tender mercies,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
who satisfies thy desire with good things, and thy youth is renewed like the eagle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Jehovah executes righteous acts, and judgments for all who are oppressed.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
He made known his ways to Moses, his doings to the sons of Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Jehovah is merciful and gracious, slow to anger, and abundant in loving kindness.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He will not always chide, nor will he keep it forever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He has not dealt with us according to our sins, nor rewarded us according to our iniquities.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
For as the heavens are high above the earth, so great is his loving kindness toward those who fear him.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as the east is from the west, so far has he removed our transgressions from us.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Like as a father pities his sons, So Jehovah pities those who fear him.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For he knows our frame. He remembers that we are dust.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
As for man, his days are as grass, as a flower of the field, so he flourishes.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
For the wind passes over it, and it is gone, and the place thereof shall know it no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But the loving kindness of Jehovah is from everlasting to everlasting upon those who fear him, and his righteousness to son's sons,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
to such as keep his covenant, and to those who remember his precepts to do them.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Jehovah has established his throne in the heavens, and his kingdom rules over all.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bless Jehovah, ye his agents, who are mighty in strength, who fulfill his word, hearkening to the voice of his word.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bless Jehovah, all ye his hosts, ye ministers of his, who do his pleasure.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bless Jehovah, all ye his works in all places of his dominion. Bless Jehovah, O my soul.