< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Maombi ya mtu aliyechoka. Anapoteseka na kumimina malalamiko yake kwa Bwana. Ee Bwana, usikie maombi yangu, kilio changu cha kuomba msaada kikufikie.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Usinifiche uso wako ninapokuwa katika shida. Unitegee sikio lako, ninapoita, unijibu kwa upesi.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Kwa kuwa siku zangu zinatoweka kama moshi, mifupa yangu inaungua kama kaa la moto.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Moyo wangu umefifia na kunyauka kama jani, ninasahau kula chakula changu.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Kwa sababu ya kusononeka kwangu kwa uchungu, nimebakia ngozi na mifupa.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Nimekuwa kama bundi wa jangwani, kama bundi kwenye magofu.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Nilalapo sipati usingizi, nimekuwa kama ndege mpweke kwenye paa la nyumba.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Mchana kutwa adui zangu hunidhihaki, wale wanaonizunguka hutumia jina langu kama laana.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Ninakula majivu kama chakula changu na nimechanganya kinywaji changu na machozi
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
kwa sababu ya ghadhabu yako kuu, kwa maana umeniinua na kunitupa kando.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Siku zangu ni kama kivuli cha jioni, ninanyauka kama jani.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Lakini wewe, Ee Bwana, umeketi katika kiti chako cha enzi milele, sifa zako za ukuu zaendelea vizazi vyote.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Utainuka na kuihurumia Sayuni, kwa maana ni wakati wa kumwonyesha wema; wakati uliokubalika umewadia.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Kwa maana mawe yake ni ya thamani kwa watumishi wako, vumbi lake lenyewe hulionea huruma.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Mataifa wataogopa jina la Bwana, wafalme wote wa dunia watauheshimu utukufu wako.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Kwa maana Bwana ataijenga tena Sayuni na kutokea katika utukufu wake.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Ataitikia maombi ya mtu mkiwa, wala hatadharau hoja yao.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Hili na liandikwe kwa ajili ya kizazi kijacho, ili taifa litakaloumbwa baadaye waweze kumsifu Bwana:
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
“Bwana alitazama chini kutoka patakatifu pake palipo juu, kutoka mbinguni alitazama dunia,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
kusikiliza vilio vya uchungu vya wafungwa na kuwaweka huru wale waliohukumiwa kufa.”
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Kwa hiyo jina la Bwana latangazwa huko Sayuni na sifa zake katika Yerusalemu,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
wakati mataifa na falme zitakapokusanyika ili kumwabudu Bwana.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Katika kuishi kwangu alivunja nguvu zangu, akafupisha siku zangu.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Ndipo niliposema: “Ee Mungu wangu, usinichukue katikati ya siku zangu; miaka yako inaendelea vizazi vyote.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Hapo mwanzo uliweka misingi ya dunia, nazo mbingu ni kazi ya mikono yako.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Hizi zitatoweka, lakini wewe utadumu, zote zitachakaa kama vazi. Utazibadilisha kama nguo nazo zitaondoshwa.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Lakini wewe, U yeye yule, nayo miaka yako haikomi kamwe.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Watoto wa watumishi wako wataishi mbele zako; wazao wao wataimarishwa mbele zako.”