< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Oración de alguien que está sufriendo y está cansado, encomendando sus problemas al el Señor. Por favor, Señor, ¡escucha mi oración! ¡Escucha mi clamor a ti pidiendo ayuda!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
¡No escondas tu rostro de mí en mis horas de angustia! Vuélvete y escúchame, y responde rápido cuando llamo.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
¡Porque mi vida está desapareciendo como el humo; siento como si mi cuerpo estuviera en llamas!
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
¡Soy como la grama que se secó, y se marchitó, ya ni recuerdo cuándo debo comer!
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Mis gemidos me han revestido; mis huesos se dejan ver a través de mi piel.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Soy como un búho del desierto, como una pequeña lechuza entre las ruinas.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
No puedo conciliar el sueño. Soy como un pájaro solitario en la azotea.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Mis enemigos se mofan de mí. Se burlan y maldicen en mi nombre.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Las cenizas son mi comida; mis lágrimas gotean encima de mi bebida,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
Por tu hostilidad y tu enojo, me recogiste y me volviste arrojar bien lejos.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Mi vida se desvanece lentamente como sombras nocturnas, me estoy marchitando como la grama.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Pero tú, Señor, reinarás para siempre, tu gloria perdurará por todas las generaciones.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Te levantarás y tendrás piedad de Jerusalén, porque es tiempo de que seas gentil con la ciudad, el tiempo ha llegado.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Porque las personas que te siguen aman sus piedras; ¡valoran incluso su polvo!
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Entonces las naciones te temerán, Señor; todos los reyes de la tierra se postrarán ante tu presencia.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Porque el Señor reconstruirá Jerusalén; y aparecerá con gloria.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Atenderá las oraciones de los desamparados; no ignorará sus pedidos.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Que esto sea recordado por las generaciones futuras, para que las personas que aún no han nacido alaben al Señor:
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Porque él mira desde los cielos, desde lo más alto de su lugar santo; él observa a la tierra desde su trono,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
para responder a los lamentos de los prisioneros, para liberar a los hijos de la muerte.
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Y como resultadoj la maravillosa naturaleza del Señor será alabada en Jerusalén con alabanzas,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
cuando las personas de todos los reinos se reúnan para adorar al Señor.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Pero, en cuanto a mí, él me quitó la salud cuando era joven, acortando mi vida.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Clamé al Señor, “Mi Dios, ¡No me arrebates mi vida mientras aún soy joven! Tú eres el único que vive para siempre.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Hace mucho tiempo creaste la tierra; hiciste los cielos.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Y ellos llegarán a su fin, pero tú no. Todos ellos se desgastarán como la ropa, y tú los cambiarás y los tirarás.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Pero tú eres el único que vive para siempre; tus años nunca llegarán a un fin.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Nuestros hijos vivirán contigo, y los hijos de nuestros hijos crecerán en tu presencia”.

< Zabura 102 >