< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Usliši mojo molitev, oh Gospod in moje vpitje naj pride do tebe.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Svojega obraza ne skrivaj pred menoj na dan, ko sem v stiski; nagni k meni svoje uho. Na dan, ko kličem, mi naglo odgovori.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Kajti moji dnevi so použiti kakor dim in moje kosti so sežgane kakor ognjišče.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Moje srce je prizadeto in ovenelo kakor trava, tako da pozabljam jesti svoj kruh.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Zaradi glasu mojega stokanja se moje kosti lepijo na mojo kožo.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Podoben sem pelikanu iz divjine; podoben sem sovi v puščavi.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Bedim in sem kakor vrabec sam na strehi.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Moji sovražniki me ves dan grajajo in tisti, ki so besni name, prisegajo zoper mene.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Kajti pepel sem jedel kakor kruh in svojo pijačo sem mešal z jokom,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
zaradi tvojega ogorčenja in tvojega besa, kajti vzdignil si me in me vrgel dol.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Moji dnevi so kakor senca, ki se zmanjšuje in izsušen sem kakor trava.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Toda ti, oh Gospod, boš ostal na veke in tvoj spomin vsem rodovom.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Vstal boš in imel usmiljenje do Siona, kajti čas, da mu [izkažeš] naklonjenost, da, določeni čas je prišel.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Kajti tvoji služabniki uživajo v njegovih kamnih in so naklonjeni njegovemu prahu.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Tako se bodo pogani bali Gospodovega imena in vsi kralji zemlje tvoje slave.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Ko bo Gospod zgradil Sion, se bo prikazal v svoji slavi.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Upošteval bo molitev revežev in ne bo preziral njihove molitve.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
To bo zapisano za prihajajoči rod; in ljudstvo, ki bo ustvarjeno, bo hvalilo Gospoda.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Kajti on je pogledal dol iz višine svojega svetišča, z nebes je Gospod pogledal zemljo,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
da usliši stokanje jetnika, da osvobodi tiste, ki so določeni za smrt,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
da oznani Gospodovo ime na Sionu in njegovo hvalo v Jeruzalemu,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
ko se zberejo skupaj ljudstva in kraljestva, da služijo Gospodu.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Oslabil je mojo moč na poti, skrajšal je moje dneve.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Rekel sem: »Oh moj Bog, ne odstrani me v sredi mojih dni; tvoja leta so skozi vse rodove.«
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Od davnine si položil temelj zemlji in nebo je delo tvojih rok.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Ta [dva] bosta izginila, toda ti boš ostal. Da, vsa se bosta postarala kakor obleka; zamenjal ju boš kakor suknjo in bosta zamenjani,
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
toda ti si isti in tvoja leta ne bodo imela konca.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Otroci tvojih služabnikov bodo nadaljevali in njihovo seme bo utrjeno pred teboj.