< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Senhor, ouve a minha oração, e chegue a ti o meu clamor.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Não escondas de mim o teu rosto no dia da minha angustia, inclina para mim os teus ouvidos; no dia em que eu clamar, ouve-me depressa.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Porque os meus dias se consomem como o fumo, e os meus ossos ardem como um lar.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
O meu coração está ferido e secco como a herva, pelo que me esqueço de comer o meu pão
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Por causa da voz do meu gemido os meus ossos se apegam á minha pelle.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Sou similhante ao pelicano no deserto: sou como um mocho nas solidões.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Vigio, sou como o pardal solitario no telhado.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Os meus inimigos me affrontam todo o dia: os que se enfurecem contra mim teem jurado.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Pois tenho comido cinza como pão, e misturado com lagrimas a minha bebida.
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
Por causa da tua ira e da tua indignação, pois tu me levantaste e me arremeçaste.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Os meus dias são como a sombra que declina, e como a herva me vou seccando.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Mas tu, Senhor, permanecerás para sempre, e a tua memoria de geração em geração.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Tu te levantarás e terás piedade de Sião; pois o tempo de te compadeceres d'ella, o tempo determinado, já chegou.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Porque os teus servos teem prazer nas suas pedras, e se compadecem do seu pó.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Então as nações temerão o nome do Senhor, e todos os reis da terra a tua gloria.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Quando o Senhor edificar a Sião, apparecerá na sua gloria.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Elle attenderá á oração do desamparado, e não desprezará a sua oração.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Isto se escreverá para a geração futura; e o povo que se crear louvará ao Senhor.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Pois olhou desde o alto do seu sanctuario, desde os céus o Senhor contemplou a terra.
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
Para ouvir o gemido dos presos, para soltar os sentenciados á morte;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Para annunciarem o nome do Senhor em Sião, e o seu louvor em Jerusalem;
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
Quando os povos se ajuntarem, e os reinos, para servirem ao Senhor.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Abateu a minha força no caminho; abreviou os meus dias.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Dizia eu: Meu Deus, não me leves no meio dos meus dias, os teus annos são por todas as gerações.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Desde a antiguidade fundaste a terra: e os céus são obra das tuas mãos.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Elles perecerão, mas tu permanecerás: todos elles se envelhecerão como um vestido; como roupa os mudarás, e ficarão mudados.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Porém tu és o mesmo, e os teus annos nunca terão fim.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Os filhos dos teus servos continuarão, e a sua semente ficará firmada perante ti.

< Zabura 102 >