< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Bøn av ein arming, når han vanmegtast og let sitt klagemål strøyma fram for Herren. Herre, høyr mi bøn, og lat mitt rop koma fram til deg!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Løyn ikkje ditt andlit for meg den dagen eg er i naud! Bøyg ditt øyra til meg! Den dagen eg ropar, svara meg snart!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
For dagarne mine hev fare burt som ein røyk, og mine bein er som glødde i eld.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Mitt hjarta er solstukke og visnar som gras, for eg hev gløymt å eta brødet mitt.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
For mi høgmælte stynjing heng beini fast ved kjøtet mitt.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Eg likjest pelikanen i øydemarki, eg er som ula på aude stader.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Eg lyt vaka og vera som ein einsleg fugl på taket.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Heile dagen spottar mine fiendar meg, dei som reint er ville mot meg, sver ved meg.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
For eg et oska som brød, og drykken min blandar eg med gråt
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
for din vreide og din harm skuld, for du hev teke meg upp og kasta meg burt.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Mine dagar er som ein skugge når han lengjest, og eg visnar som gras.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Men du, Herre, sit i all æva, og ditt minne varer frå ætt til ætt.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Du vil standa upp, du vil miskunna Sion, for det er tid til å vera nådig mot henne, ja, timen er komen.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For dine tenarar hev godhug for steinarne hennar, og dei ynkast yver hennar grus.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Og heidningar skal ottast Herrens namn, og alle kongar på jordi di æra.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
For Herren hev bygt upp att Sion, han hev synt seg i si æra;
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
han hev vendt seg til bøni frå dei hjelpelause, og han hev ikkje vanvyrdt deira bøn.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Dette skal verta uppskrive for den komande ætti, og det folket som vert skapt, skal lova Herren,
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
for han hev set ned frå si heilage høgd, Herren hev frå himmelen skoda på jordi
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
og vil høyra sukken frå den bundne og løysa ut daudens born,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
so dei i Sion skal forkynna Herrens namn og hans pris i Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
når folkeslag kjem i hop og kongerike til å tena Herren.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Han hev bøygt mi kraft på vegen, han hev korta av mine dagar.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Eg segjer: Min Gud, tak meg ikkje burt midt i mine dagar! Frå ætt til ætt varer dine år.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Fordom grunnfeste du jordi, og himmelen er verk av dine hender.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Dei skal forgangast, men du stend; alle skal dei eldast som eit klæde, som ein klædnad skifter du deim, og dei vert umskifte;
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
men du er den same, og dine år tek aldri ende.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Borni åt dine tenarar skal bu i ro, og deira avkjøme skal standa trygt for di åsyn.